Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-25@10:56:10 GMT

An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara

Published: 23rd, March 2025 GMT

An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ilorin, karkashin jagorancin Mai shari’a Abimbola Awogboro ta yanke wa Musa Buba hukuncin daurin sa’o’i 300 da hidimar al’umma, bisa samunsa da laifin gudanar da harkokin kasuwanci na canji ba tare da wani cikakken lasisi ba.

Hakazalika, alkalin ya kuma yanke hukuncin daure wani Akinwale Olamilekan daga Owena Ijesha a karamar hukumar Oriade ta jihar Osun, daurin sa’o’i 300 (dari uku) da yiwa al’ummar hidima na tsawon sa’o’i biyar a kowace rana ba tare da zabin biyan tara ba, bayan da ya same shi da laifin aikata laifukan da suka shafi yanar gizo wato walawala ko yahoo boyi.

Hukumar dake yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta gurfanar da Musa da Akinwale a gaban kotu a ranar Alhamis, 20 ga Maris, 2025.

Ana tuhumar Musa Buba a wani lokaci a watan Yulin 2024 a kasuwar Chikanda, gundumar Yashikira, a karamar hukumar Baruten, jihar Kwara, yana gudanar da harkokin wata cibiyar hada-hadar kudi, Bureau De Change Business, ba tare da wani sahihin lasisi da babban bankin Najeriya ya bayar ba.

Laifin ya ci karo da Sashe na 57 (1) & (2) na Dokar Bankunan da Sauran Cibiyoyin Kudi, 2020, kuma ana hukunta shi a karkashin sashe na 57(5) (b) na wannan dokar.”

A cikin tuhumar da ake wa Akinwale Olamilekan (Alias: Mary Williams), an zarge shi da samun wani lokaci a watan Nuwamba 2024, da damfara da wata Mary Williams ta hanyar sakon karta kwana na iMessage asusu don karbar kudi $950 (Dalar Amurka Dari Tara da 55) daga wani Mark Durham.

Laifin ya sabawa sashe na 22 (2) (b) (ii) na laifukan Intanet (Hana, Rigakafin, da sauransu) Doka kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin sashe na 22 (2) (b) (iv) na wannan Dokar.

Wadanda ake tuhumar sun amsa laifinsu.

 

Da yake tabbatar da gaskiyar lamarin, hujjojin da masu gabatar da kara karkashin jagorancin Andrew Akoja suka gabatar da kuma kararrakin wadanda ake tuhumar, mai shari’a Awogboro ya yanke musu hukunci daidai laifin da suka aikata.

Baya ga hukuncin, kotun ta umurci Musa Buba da ya bata kudaden da suka kai CFA 409,500 da kuma Naira 1,973,200 (Miliyan Daya, Dari Tara da Dubu Saba’in da Uku, Naira Dari Biyu Kadai) ga gwamnatin tarayya.

Hakazalika, Alkalin ya umarci Akinwale da ya ba Gwamnatin Tarayya dalar Amurka $450 (Dalar Amurka dari hudu da hamsin), da kuma wata wayar iphone 12 Pro Max da ya yi amfani da ita wajen aikata laifin.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Damfara Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli

A cewar takardun kotun, gwamnonin suna neman a bayyana cewa, hukuncin da shugaban kasa ya zartar ya saɓa wa sashe na 1 (2), 5 (2), da 305 na kundin tsarin mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima).

 

Sun kuma kara da cewa, shugaban kasa ba shi da wani iko ko kadan na dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da mataimakin gwamnan wata jiha a tarayyar Nijeriya bisa fakewa da dokar ta-ɓaci.

 

Gwamnonin kuma suna kalubalantar amincewa da dokar ta-ɓaci da majalisar dokokin kasar ta yi, suna masu cewa, yin amfani da kuri’a jin ra’ayi ta baki ya saɓawa kundin tsarin mulkin kasar, saboda dokar ta ce, dole sai an samu mafi rinjayen kuri’a biyu cikin uku na dukkan ‘yan majalisar.

 

A cikin jawabin da suka gabatar wa kotun, masu shigar da kara sun kara da cewa, dokar ta-ɓacin ba ta cika ka’idojin tsarin mulki da sashi na 305 ya gindaya ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • An yi wa wata karya tiyatar ceton rai