Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
Published: 23rd, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta kama wasu matasa huɗu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kashe wani yaro ɗan shekara shida, Shuaibu Safiyanu, a ƙauyen Sade da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.
Aminiya ta ruwaito cewar mahaifin yaron, Safiyanu Abdullahi ne, ya sanar da Sarkin garinsu, Musa Isah, cewa a ranar 20 ga watan Maris, 2025, ɗansa ya ɓace.
Washegari, wani ya kira shi a waya yana neman kuɗin fansa.
Da farko, ya nemi miliyan uku (₦3,000,000), amma daga baya suka rage zuwa Naira dubu ɗari biyu (₦200,000).
A ranar 21 ga watan Maris, aka gano gawar yaron a cikin daji, an ɗaure masa wuya da igiya.
Nan take aka kai shi asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yi masa jana’iza.
Kakakin ’yan sandan Jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an su suka fara bincike.
Sun fara binciken ne daga wajen POS da ke kusa da inda aka buƙaci a biya kuɗin fansar.
A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka.
An gano cewa lambar wayarsa ce aka yi amfani da ita wajen kiran mahaifin yaron.
Sannan ’yan sanda sun gano asusun bankin da aka bayar don biyan kuɗin fansar: Lambar asusu: 0145285130 Sunan mai asusu: Ozochikelu Samson Banki: Union Bank PLC
Bayan kama Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozochikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yadda za a sace yaron.
Ya kuma ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi), mai shekara 25, da Musa Usman (Kala), mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.
A halin yanzu, ’yan sanda suna tsare da su, kuma ana ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka (SCID).
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya tabbatar da cewa za su tabbatar da an yi adalci.
Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai, tare da sanar da su duk wani abun zargi ta layin kiran wayar gaggawa 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.
Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Garkuwa yaro mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ilorin, karkashin jagorancin Mai shari’a Abimbola Awogboro ta yanke wa Musa Buba hukuncin daurin sa’o’i 300 da hidimar al’umma, bisa samunsa da laifin gudanar da harkokin kasuwanci na canji ba tare da wani cikakken lasisi ba.
Hakazalika, alkalin ya kuma yanke hukuncin daure wani Akinwale Olamilekan daga Owena Ijesha a karamar hukumar Oriade ta jihar Osun, daurin sa’o’i 300 (dari uku) da yiwa al’ummar hidima na tsawon sa’o’i biyar a kowace rana ba tare da zabin biyan tara ba, bayan da ya same shi da laifin aikata laifukan da suka shafi yanar gizo wato walawala ko yahoo boyi.
Hukumar dake yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta gurfanar da Musa da Akinwale a gaban kotu a ranar Alhamis, 20 ga Maris, 2025.
Ana tuhumar Musa Buba a wani lokaci a watan Yulin 2024 a kasuwar Chikanda, gundumar Yashikira, a karamar hukumar Baruten, jihar Kwara, yana gudanar da harkokin wata cibiyar hada-hadar kudi, Bureau De Change Business, ba tare da wani sahihin lasisi da babban bankin Najeriya ya bayar ba.
Laifin ya ci karo da Sashe na 57 (1) & (2) na Dokar Bankunan da Sauran Cibiyoyin Kudi, 2020, kuma ana hukunta shi a karkashin sashe na 57(5) (b) na wannan dokar.”
A cikin tuhumar da ake wa Akinwale Olamilekan (Alias: Mary Williams), an zarge shi da samun wani lokaci a watan Nuwamba 2024, da damfara da wata Mary Williams ta hanyar sakon karta kwana na iMessage asusu don karbar kudi $950 (Dalar Amurka Dari Tara da 55) daga wani Mark Durham.
Laifin ya sabawa sashe na 22 (2) (b) (ii) na laifukan Intanet (Hana, Rigakafin, da sauransu) Doka kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin sashe na 22 (2) (b) (iv) na wannan Dokar.
Wadanda ake tuhumar sun amsa laifinsu.
Da yake tabbatar da gaskiyar lamarin, hujjojin da masu gabatar da kara karkashin jagorancin Andrew Akoja suka gabatar da kuma kararrakin wadanda ake tuhumar, mai shari’a Awogboro ya yanke musu hukunci daidai laifin da suka aikata.
Baya ga hukuncin, kotun ta umurci Musa Buba da ya bata kudaden da suka kai CFA 409,500 da kuma Naira 1,973,200 (Miliyan Daya, Dari Tara da Dubu Saba’in da Uku, Naira Dari Biyu Kadai) ga gwamnatin tarayya.
Hakazalika, Alkalin ya umarci Akinwale da ya ba Gwamnatin Tarayya dalar Amurka $450 (Dalar Amurka dari hudu da hamsin), da kuma wata wayar iphone 12 Pro Max da ya yi amfani da ita wajen aikata laifin.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU