Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
Published: 23rd, March 2025 GMT
Kimanin shekaru 12 da suka wuce, wato a ranar 23 ga watan Maris din shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, a karon farko, yayin da yake jawabi a wata jami’a dake birnin Moscow na kasar Rasha. Asalin tunanin ya shafi al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya bukaci a samu jituwa, da daidaito tsakanin al’ummu daban daban, da tsakanin dan Adam da muhallin halittu.
Bisa tushen tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya ne, kasar Sin ta gabatar da karin shawarwari, irinsu Ziri Daya da Hanya Daya, da wadanda suka shafi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar al’adu a duniya, ta yadda za a samu damar aiwatar da tunanin a harkokin dan Adam na fannoni daban daban.
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba nanata cewa, yayin da ake aiwatar da tunanin raya al’ummar dan Adam, ba za a ce wasu al’adu sun fi wasu ba, kuma ba za a nemi maye gurbin wani tsarin al’umma da wani na daban ba. Maimakon haka, abin da za a yi shi ne hakuri da bambancin kasashe daban daban, ta fuskokin tsarin al’umma, da al’adu, da matsayin ci gaban tattalin arziki, sa’an nan a raba riba, da hakki, da nauyin aiki a tsakanin su, don tabbatar da makoma mai haske ta al’ummar dan Adam. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: al ummar dan Adam
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
Kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas ta fitar da wata sanarwa dangane da shahadar Salah al-Bardawil, mamba a ofishin siyasa na kungiyar kuma wakilin majalisar dokokin Falasdinu.
A rahoton tashar Al-Alam, bayanin Hamas yana cewa: Dr. Salah Al-Bardawil, wanda ya yi fice a fagen siyasa, kafofin watsa labarai, da fagage na kasa da kasa, kuma ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan kusoshin Hamas, wanda yake a kan gaba wajen gwagwarmaya da sadaukarwa, ya yi shahada a kan tafarkin gaskiya.
Bayanin ya ci gaba da cewa: Bai taba gazawa wajen gudanar da ayyukansa na jihadi da hidima ga al’ummar Palastinu ba, ya kuma ci gaba da yin gwagwarmaya kan turba ta gaskiya da neman ‘yanci har zuwa karshen rayuwarsa.
Hamas ta jaddada cewa, jinin Dakta Al-Bardawil da matarsa da sauran shahidai wata fitila ce da za ta haskaka hanyar samun ‘yanci ga al’ummar Falastinu, kuma laifuffukan makiya ba za su taba raunana azama da jajircewar ‘yan gwagwarmaya a Falastinu ba.
A karshen wannan sanarwa da ta fitar a wannan Lahadi 23 ga Maris, 2025, kungiyar Hamas ta yi fatan samun rahama da aljannah ga Dr. Salah Bardawil da matarsa, tare da sauran wadanda suka yi shahada a kan tafarkin gaskiya.
Salah Al-Bardawil da matarsa sun yi shahada ne a daren ranar 23 ga watan Ramadan, bayan wani hari da yahudawan sahyuniya suka kai a kan tantin su da suke a yankin Al-Mawasi da ke yammacin birnin Khan Yunus.
Wannan harin dai wani bangare ne na kisan gilla da yahudawan Haramtacciyar Kasar Isra’ila suke ci gaba da yi kan al’ummar Gaza marasa kariya, tare da samun cikakken goyon baya da karfin gwiwa da dukkanin taimako kan hakan daga gwamnatin kasar Amurka.