Aminiya:
2025-03-25@13:55:49 GMT

Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa

Published: 23rd, March 2025 GMT

Gwamnonin Arewa sun aike wa Gwamna Dikko Umar Radda na Jihar Katsina, saƙon ta’aziyya game da rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Safara’u Umaru Baribari, wadda ta rasu tana da shekaru 93.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana Hajiya Safara’u a matsayin uwa mai tausayi da riƙon gaskiya, wadda ta rayu bisa turbar Allah da hidima wa al’umma.

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, Gwamna Yahaya, ya iyalanta da shugabanni za su yi kewarta.

Ya kuma buƙaci Gwamna Radda da iyalansa da su ci gaba da girmama tarihinta ta hanyar riƙe kyawawan halayenta na gaskiya da nagarta.

Gwamnan Gombe, ya kuma miƙa ta’aziyyar gwamnatinsa da mutanen jiharsa, ta hanyar addu’ar Allah Ya gafarta mata, Ya kuma sa Aljanna Firdausi ta zama makomarta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dikko Umar Radda Gwamna Inuwa Yahaya Gwamnonin Arewa Mahaifiya rasuwa ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Wasu fusatattun matasa sun daka wawa kan kayan abincin tallafin azumi da ɗan Shugaba Nijeriya, Seyi Tinubu zai raba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa duk da cewa bai kai ga zuwa jihar ta Gombe ba, amma kayan abinci da zai raba tuni sun isa jihar.

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ya nuna matasan na wawason katan-katan na kayan abinci daga kan wata mota da ke tsaye a bakin titi.

An hangi matasan na jefa wa waɗanda ke ƙasa kayan abincin — inda suke karɓa su kama gabansu.

Kayan abincin sun haɗa da buhunan shinkafa da sikari da mai da taliya da kuma gishiri.

Yayin da tuni an raba ɗaya daga cikin motocin ɗauke da kayan abincin, matasan sun tare guda inda suka yi wawushe komai da ke cikinta.

A bayan nan dai ɗan gidan shugaban ƙasar na shawagi a wasu jihohin arewacin Nijeriya, inda yake haɗuwa da mazauna jihohin da kuma shugabannin siyasa wajen buɗa-baki.

A yayin waɗannan ziyarce-ziyarce ne kuma ɗan shugaban ƙasar yake ƙaddamar da rabon tallafin abinci ga mabuƙata da albarkacin watan azumi.

Sai dai wannan lamari na ci gaba da janyo cece-kuce a faɗin ƙasar, a yayin da wasu ke yabawa wasu ko kushe suke yi.

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi Allah wadai da rabon abincin da ɗan shugaban ƙasar ya yi a yankin Arewa, yana bayyana hakan a matsayin wani nau’i na rashin mutunta al’adun Arewa.

A cikin wani bidiyo da karaɗe shafukan sada zumunta, Lamido ya bayyana hakan a yayin wani taron buɗa-baki na mambobin jam’iyyar PDP da ya gudana a garin Bamaina da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.

A makon jiya ne ɗan gwamnan Bauchi, Shamsuddeen Bala Mohammed, ya yi kira ga Seyi Tinubu da ya yi amfani da ziyararsa don tallafa wa matasan jihar.

Shamsuddeen Bala Mohammed ya ce bai kamata a mayar da matasan Bauchi kamar mabarata ba, sai dai a ba su damar dogaro da kansu ta hanyar ayyukan yi da horo na musamman.

Shamsuddeen ya bayyana cewa matasan Bauchi sun fi buƙatar ayyukan yi da jari, ba kayan abinci kawai ba.

Ya buƙaci a ba su tallafi kamar Keke NAPEP, kuɗin kafa kasuwanci, da kuma horo a fannin sadarwar zamani da cinikayyar kirifto domin inganta rayuwarsu.

Ɗan gwamnan na Bauchi ya ce yana da kyau a koya wa matasa yadda za su dogara da kansu fiye da ba su abinci da zai kare a rana ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Sule Lamido Ya Soki Rabon Abinci da Seyi Tinubu Ya Yi A Arewa
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar