Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
Published: 23rd, March 2025 GMT
Shugaba hukumar makashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bada sanarwan cewa a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa. Yace hukumarsa za ta kaddamar da sabbin magunguna da ta samar tare da amfani da makamashin Nukliya, a dai dai na ranar makamashin Nukliya ta kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto Islami yana fadar haka a yau Lahadi, ya kuma kara da cewa wannan ci gaban kari ne, kan ci gaban da kasar ta samu a wannan fannin, wanda kuma zai kara kyautata bangaren lafiya na kasar sannan ya zama hanyar samar da kudade ga kasar.
Shugaba hukumar makamashin nukliya ta Iran ya kara da cewa a cikin shekarar Iraniyawa wanda ya kara kadai kasar ta samar da sabbin ci gaba kimani 100 tare da amfani da makamashin nucliya, kuma tana son nan da shekara ta 2040 masana’antar makamashin nukliya ta kasar Iran zata shiga cikin masana’antun makamshin nukliya mafi girma a duniya.
Ana saran shugaba Pezeshkiyan zai halarci taron kaddamarda wadandan kayakin ci gaba da aka samu a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa.
Sannan Iran ta dage kan cewa shirinta na makamashin Nukliya na zaman lafiya ne, sabanin abinda kasashen yamma musamman Amurka take zargin kasar na cewa shirin ya wuce na zaman lafiya.
Sai dai kakakin Fadar Krimlin na kasar Rasha Dmitry Medbedev ya bayyana a makon da ya gabata kan cewa shirin makamashin Nukliya na kasar Iran na zaman lafiya ne.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin Nukliya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya musanta zargin kasar Amurka na cewa wasu jiragen ruwan JMI suna amfani da tudan kasar Iraqi sun kai kawo a ruwayen yankin.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fadawa Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran, kan cewa Aragchi yana fadar haka ne a jiya litinin, a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Iraki Fu’ad Hussain.
Kafin haka ministan ya nakalto korafin da jami’an gwamnatin kasar Amurka suka gabatarwa gwamnatin kasar Iraki na cewa jiragen ruwan kasar Iran na amfani da takardun bugi na kasar Iraki don gudanar da harkokinsu a yankin. Aragchi ya musanta hakan ya kuma kara da cewa gwamnatin kasar Amurka tana son raba JMI da dukkan kasashe makobta don cimma manufofinta na maida kasar Iran saniyar ware a duniya.
Ministocin biyu sun tattauna batun abubuwan da suke faruwa a yankin Asiya ta kudu wadanda suka hada da bautun kissan kiyashin da yahudawan sahyoniyya suke yi a kasar Falasdinu da aka mamaye.
A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Iraqi ya ce kasar Iraki bada cikin kwancen masu gwagwarmaya a yankin. Wannan kamar yadda kowa ya sani bukata ce daga kasar Amurka na gwamnatin kasar Iraki ta fidda kanta daga kawancen gwagwarmaya wanda kasar Iran take jagoranta a yankin.