Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
Published: 24th, March 2025 GMT
4 – Kar ki kasance kullum a cikin bacin rai ko fushi da mijinki, domin fushi kofa ce ta kowane sharri.
5 – Kar ki kasance mai girman kai wajen bashi hakkokin zamanku, abin da yake so ko da baki so matukar bai saba wa addini ba ki yi masa.
6 Ki nuna wa mijinki komai naki nasa ne komai nasa kuma nasa ne, ki nuna baki da iko a kai sai abin da ya yi.
7- Ki kasance mai kula da abubuwan da yake dubawa a jikinki in ya shigo gida, ina idonsa ke kallo a jikinki. Bayan kin yi kwalliya. sai a gyara masa su da kyau domin a dauke masa hankali. In kuma kin tabbatar duk lokacin da ya dawo yana neman buta ne, to ki kula da sanya ruwa a cikin butar.
8 – Ki kasan ce mai yawan godiya kan duk abin da ya kawo miki gida komai kankantar abin kar ki raina, sannan ki nuna masa kokarinsa a kan bin da ya kawo.
9 – Kar ki sake ko ki yi kasa a gwiwa wajen girmama duk wadanda kika san yana girmama su, kama daga iyaye har ‘yan uwa da abokan arzikinsa.
10- Kar ki yawaita tambayarsa daga ina kake ko me kake yi sai yanzu kake dawowa?
Ki kasance mai boye sirrinsa wajen iyayenki da sauran al’umma. 11 – Kar ki yarda duk lokacin da ya kiranki ki kawo masa wani abu ki tura wani ko wata ta kawo, ki je ki yi da kanki. Wadan abubuwa idan kika daure kina yi lallai za ki samu namiji a hannunki kamar dan jariri. Allay a ba da ikon yi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
Za a ɗauko hayar ƙwararrun sojoji daga ƙetare domin horar da sojin ƙasar aikin ƙundumbala wajen tunkarar ’yan ta’adda da kuma ƙwato mutanen da aka yi garkuwa da su a Nijeriya.
Ministan Tsaron Nijeriya, Badaru Abubakar ya sanar da haka lokacin ƙaddamar da aikin horar da sojojin 800 a Jaji da ke Jihar Kaduna.
Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDDAbubakar ya ce baya ga horaswar, gwamnati za ta samar wa dakarun kayan aiki na zamani da za su yi amfani da su wajen daƙile matsalolin tsaron da ake samu.
Ministan ya ce a karon farko, sojojin 800 za su ci gajiyar wannan horaswar, yayin da daga bisani wasu 800 kuma su biyo baya.
Badaru ya ce sun ɗauki wannan matakin ne domin tinkarar matsalar ƴan ta’adda waɗanda su ma ke sauya dabaru a kodayaushe.
Kodayake ministan bai sanar da sunayen ƙasashen da za a ɗauka hayar waɗannan zaratan sojojin ba, amma ya ce za a ɗauko su ne daga wasu ƙasashen duniya bakwai.
A zangon farko kaɗai, jimillar sojojin Nijeriya dubu 2 da 400 ne za a fara bai wa horan na musamman, kafin a tsallaka zuwa zango na biyu.
Ministan ya bayyana cewa, ana samun kwanciyar hankali a wasu yankunan ƙasar sakamakon yadda gwamnati ta duƙufa wajen magance matsalar tsaro, inda har ya ba da misali da yankin Birnin Gwari da ke Jihar Kaduna, yankin da a cewarsa, an samu zaman lafiya a yanzu.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fama da matsalar ’yan bindiga musamman a yankin arewacin Najeriya, inda suke garkuwa da jama’a domin karɓar kuɗin fansa, yayin da a wasu lokuta suke aiwatar da kisa.