An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
Published: 24th, March 2025 GMT
A yau Lahadi ne aka bude taron shekara-shekara na dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin na 2025 a nan birnin Beijing, taron da cibiyar binciken raya kasa ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta shirya tare da hadin gwiwar asusun binciken raya kasa na kasar Sin. Firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci bikin bude taron, inda ya gabatar da muhimmin jawabi, wanda a cikinsa ya jaddada aniyar kasar Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje.
Shi ma mataimakin darektan ofishin kula da harkokin yau da kullum na hukumar kudi da tattalin arziki ta kwamitin kolin JKS Han Wenxiu, wanda ya halarci taron na shekara-shekara, ya ce kasar Sin za ta dauki dukkan matakai na habaka kashe kudi, da kuma ci gaba da haifar da yanayi, ta yadda ingantaccen ci gaba da kyakkyawar rayuwa za su rika karfafar juna.
Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A ZamfaraZa a shafe kwanaki biyu ana gudanar da taron, bisa jigon “Ingiza karfin ci gaba, tare da inganta kyakkyawan ci gaban tattalin arzikin duniya”. Taron ya hallara wakilai daga manyan kamfanoni 86 na kasashe 21. A yayin taron, mahalarta na kasar Sin da na kasashen waje, za su gudanar da tarukan karawa juna sani 12, kan batutuwan da suka hada da manyan manufofi, da yin gyare-gyare, da kara yawan amfani da kayayyaki, da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da fasahar AI.
Tun lokacin da aka kaddamar da dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin a shekarar 2000, dandalin ya zama wata muhimmiyar gada da ta sa kaimi ga yaukaka tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashen duniya. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: raya kasa na na kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024
Ma’aikatar kula da albarkatun ruwa ta kasar Sin ta bayyana a jiya Juma’a cewa, fadin yankin kasar dake fama da zaizayar kasa ya ragu zuwa murabba’in kilomita miliyan 2.6019 a shekarar 2024, wanda ya samu raguwar murabba’in kilomita 25,700, idan aka kwatanta da na shekarar 2023.
Wadanann alkaluman wani bangare ne na sakamakon aikin sa ido kan zaizayar kasa a kasar Sin a shekarar 2024, wanda aka kammala a kwanan nan.
Wakilin Musamman Na Xi Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adamaWani jami’in ma’aikatar ya bayyana cewa, sakamakon da aka samu ya nuna cewa, ana samun ci gaba bisa daidaito wajen magance zaizayar kasa a kasar Sin, inda aka samu raguwar fadin yankin da ke fuskantar matsalar da ma karfin zaizayar kasa, gami da raguwar zaizayar kasa bisa dalilan ruwa da iska.
Manyan kogunan da suka hada da kogin Yangtze, Rawayen Kogi, da kogin Huaihe, sun kai kashi 73.19 cikin 100 na yankin da aka samu raguwar zaizayar kasa a fadin kasar baki daya. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp