An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
Published: 24th, March 2025 GMT
A yau Lahadi ne aka bude taron shekara-shekara na dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin na 2025 a nan birnin Beijing, taron da cibiyar binciken raya kasa ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta shirya tare da hadin gwiwar asusun binciken raya kasa na kasar Sin. Firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci bikin bude taron, inda ya gabatar da muhimmin jawabi, wanda a cikinsa ya jaddada aniyar kasar Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje.
Shi ma mataimakin darektan ofishin kula da harkokin yau da kullum na hukumar kudi da tattalin arziki ta kwamitin kolin JKS Han Wenxiu, wanda ya halarci taron na shekara-shekara, ya ce kasar Sin za ta dauki dukkan matakai na habaka kashe kudi, da kuma ci gaba da haifar da yanayi, ta yadda ingantaccen ci gaba da kyakkyawar rayuwa za su rika karfafar juna.
Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A ZamfaraZa a shafe kwanaki biyu ana gudanar da taron, bisa jigon “Ingiza karfin ci gaba, tare da inganta kyakkyawan ci gaban tattalin arzikin duniya”. Taron ya hallara wakilai daga manyan kamfanoni 86 na kasashe 21. A yayin taron, mahalarta na kasar Sin da na kasashen waje, za su gudanar da tarukan karawa juna sani 12, kan batutuwan da suka hada da manyan manufofi, da yin gyare-gyare, da kara yawan amfani da kayayyaki, da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da fasahar AI.
Tun lokacin da aka kaddamar da dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin a shekarar 2000, dandalin ya zama wata muhimmiyar gada da ta sa kaimi ga yaukaka tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashen duniya. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: raya kasa na na kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha A cikin Kasar
Labaran da suke fitowa daga kasar Ukraine sun bayyana cewa, gwamnatin kasar tana son karban iko da bututun iskar gas na kasar Rasha wanda yake yammacin kasar da Turai, wanda kuma yake kai iskar gasa zuwa kasashen Turai.
An gina bututun tun zamanin tarayyar Soviet kuma kasashen biyu suna samun kudade masu yawa daga wannan bututun.
Gwamnatin kasar Amurka dai tana son ta dawo da kudaden da ta kashewa kasar Ukraine na makamai wacce ta karba a likacin shugaban Biden. Daga cikin dai Amurka ta bukaci Ukraine ta bada ma’adinanta na kimani dalar Amurka biliyon $500.
Wasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an gwanatocin kasashen Amurka da Ukraine sun tattauna wannan batun a ranar jumma’an da ta gabata, don tattauna batun irin ma’adinan da kasar Ukraine zasu bawa Amurka saboda biyan kudaden da take binta basgi. Har’ila yau Amurkawan sun gabatar da shawarar kasashen biyu su hada giwa don samun riba tare a aikin hakar Ma’adinan.