Aminiya:
2025-03-25@20:44:20 GMT

Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba

Published: 24th, March 2025 GMT

Wata mata mai suna Krystena Murray ’yar Amurka, wadda ta ɗauki ciki tare da haife jariri namiji ba tare da sanin cewa ba ɗanta ba ne, ta fara ɗaukar matakin shari’a a kan wani asibitin da ke taimaka wa mata samun ciki ta hanyar dashen ɗantayi (IBF).

Matar tana zargin asibitin da yi mata dashen ɗantayin da ba nata ba, bayan an tilasta ta, ta mayar wa asalin iyayen jaririn ɗansu.

NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa

Krystena Murray, mazauniyar Jihar Georgia, ta ɗauki cikin ne bayan dashen ɗantayi na (IBF) da aka yi mata a asibitin masu neman haihuwa da ake kira Coastal Fertility Clinic, a watan Mayun 2023.

To amma daga baya an gano cewa, ɗantayin da ta rena a cikinta na wasu ma’auratan ne daban, kamar yadda majiyar BBC ta ruwaito. Hakan ya fito fili ne bayan da Murray ta haifi jaririn da bai yi kama da ita ko wanda ya ba ta gudumawar maniyyi ba.

Duk da haka, Madam Murray ta so a bar mata yaron, don ta ci gaba da renon sa har tsawon watanni, amma hukumomi suka bai wa ainahin iyayen dan ikon karɓen ɗansu.

A cikin wani bayani da ta sanar ta hannun lauyanta, Murray ta ce: “Na ɗauki jaririn nan a cikina, na kamu da son sa, na haife shi, sannan na shaƙu da shi sosai, irin shaƙuwa ta ɗa da uwa, amma yanzu an ƙwace shi. Ba zan taɓa fita daga wannan takaici ba.”

Murray wadda baturiya ce, ta haifi jaririn, wanda ya kasance baƙar fata a watan Disamban 2023.

Ta ƙi sanya hotunan jaririn a shafukan sada zumunta sannan ta ƙi bari ’yan uwa ko abokanta su gan shi.

Daga nan ne ta sayi abin gwajin gano halittar gado, wanda za ta iya yin gwaji a gida.

Sakamakon da ta samu a watan Janairun 2024 ya tabbatar mata cewa, jaririn ba shi da alaƙa da ita, kamar yadda ta bayyana a koken da ta rubuta a kan asibitin.

Bayan wata ɗaya, ta sanar da asibitin game da lamarin. Asibitin ya sanar da asalin iyayen jaririn, waɗanda su kuma suka kai ƙara domin karɓar ɗan nasu, lokacin da yake da wata uku a duniya.

Dole ta sa Murray ta miƙa jaririn bayan lauyoyinta sun tabbatar mata cewa, ba za ta samu nasara ba, idan ta je kotu da nufin a bar mata jinjirin.

A halin yanzu jaririn na hannun iyayensa na asali a wata jiha, inda suka sauya masa suna. Koken da Murray ta shigar ya bayyana cewa, har yanzu ba ta san ko asibitin Coastal Fertility ya bai wa wasu nata ɗantayin ne ko kuma a’a.

A wani saƙo da ya tura wa kafar talabijin ta CBS News, asibitin ya amince cewa, ya tafka kuskure, sannan ya nemi afuwa game da halin da ya jefa matar a ciki.

“Wannan ne kuskure ɗaya da muka yi, kuma bai shafi wasu mutanen da muka bai wa kulawa ba,” kamar yadda asibitin ya sanar a bayaninsa.

“A ranar da aka gano wannan kuskuren, mun sake yin nazari mai zurfi a kan ayyukanmu tare da ɗaukar matakan kariya domin kare masu zuwa neman magani a wurinmu ta yadda ba za a sake samun irin haka ba.”

A shekarun baya-bayan nan an shigar da ƙararrakin asibitocin maganin haihuwa da dama kan yin kuskure wajen dashen ɗantayin.

Dashen IBF wani tsari ne da ake haɗa ƙwan haihuwar mace da maniyyin namiji a kwalba kafin a dasa ɗantayin a cikin mahaifar mace domin reno a matsayin juna-biyu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Yemen sun kara kai hare-hare goyan bayan Falasdinu

Dakarun sojin Yaman sun ce sun kara kai hare-hare na nuna kyama ga Isra’ila da Amurka a matsayin nuna goyan baya a kan zirin Gaza.

Kakakin rundunar Yahya Saree ya ce a daren jiya litinin sojojin na Yaman sun kai hari filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion na Isra’ila da makami mai linzami guda biyu da suka hada da Zulfiqar mai gudun tsiya.

Ya kara da cewa hare-haren na goyon bayan Falasdinawa ne a Gaza.

Saree ya yi nuni da cewa, dakarun kasar Yemen sun kuma kai hari kan jirgin yakin Amurka Harry S.

Saree ya ce harin da aka kai kan jiragen ruwan yakin Amurka shi ne irinsa na biyu cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Ya ce an kai harin ne domin mayar da martani ga hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar ta Yemen.

Saree ya kuma jaddada cewa za a ci gaba da gudanar da ayyukan adawa da Isra’ila har sai an daina ta’addancin gwamnatin tare da dage killacewar da aka yi wa Gaza.

A ranar 15 ga Maris, Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama da ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar Yemen 53.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • Dakarun Yemen sun kara kai hare-hare goyan bayan Falasdinu
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
  • Yadda ake noman gurjiya
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe