HausaTv:
2025-03-26@14:42:38 GMT

UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba

Published: 24th, March 2025 GMT

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya sanar da cewa, yara a Gaza suna fuskantar matsakar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba a kan kananan yara.

“Ba mu da wani bayani a tarihin wannan zamani dangane da ke bukatar tallafin lafiyar kwakwalwa kamar yaran Gaza,” in ji mai magana da yawun UNICEF James Elder a wani taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.

Sannan kuma jami’in  ya yi Allah wadai da tauye hakkin yara da ake yi da gangan a Gaza, ya kuma bukaci masu karfin fada a ji a duniya da su dauki mataki.

Ya kara da cewa an toshe alluran rigakafi 180,000 na rigakafin yara masu mahimmanci, da na’urorin saka jariran da ba su kai ga lokacin haihuwa ba, inda Isra’ila ta hana shigar da wadannan kayayyakia  cikin yankunan zirin gaza.

Babban jami’in na UNICEF ya ce, daukar irin wadannan matakana  kan yara yana a matsayin babban laifi wanda ka iya zama laifin yaki bisa dokoki na kasa d akasa.

A kan haka ya kara jaddada kiransa ga kasashe masu karfin fada a ji da su sauke nauyin da ya rataya a kansu kan batun Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla

Kungiyar da ke sa ido da kare hakkin dan adam ta Syria (SOHR) ta fitar da fayafan bidiyo guda hudu da ke dauke da hotunan azabtarwa da kisa da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin kasar  karkashin kungiyar Tahrir Sham  suke aiwatarwa a kan fararen hula tsiraru marasa rinjaye a kasar.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayyana a ranar Lahadi cewa, ta samu faifan bidiyo guda hudu ne da ke nuna yadda ake aiwatar da hukuncin kisa kan wasu matasa da ba sa dauke da makamai daga ‘yan Alawiyya, da jami’an tsaro suka aiwatar a kauyen al-Shir da ke yankin Latakia a ranar 7 ga watan Maris.

A cewar kungiyar, faifan bidiyon ya kara tabbatar da yadda aka aiwatar da kisan gillar da aka yi a yankunan gabar tekun Syria da kuma wadanda suka aikata hakan a kan fararen hula.

A cikin faifan bidiyo na farko ya nuna wasu matasa biyu sun durkusa a kasa yayin da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria  suke zaginsu tare da lakada musu matsanancin duka, duk kuwa da ikirarin da suka yi na cewa ba su aikata wani laifi ba.

A cikin wani faifan bidiyo na biyu, an nuna yadda aka azabtar da wasu fararen hula hudu  ciki har da tsofaffi biyu, da kuma tilasta wa daya daga cikinsu sumbaci takalmin wani jami’in tsaro.

Kaset na uku ya nuna irin mumunan duka da aka yi wa fararen hula da bindigogi da karafa kafin daga baya kuma duk aka kashe su.

Dukkanin wadanda suka aikata wadannan munannan laifuka dai sabbin jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da kungiyar Tahrir Sham mai dangantaka da kungiyar Alqaida ta kafa a Syria bayan hambarar da gwamnatin Bashar Assad.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • Kamfanin Apple Ya Sanar Da Zuba Sabon Jari A Fannin Samar Da Makamashi Mai Tsafta A Sin
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara