HausaTv:
2025-03-25@20:48:59 GMT

Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya

Published: 24th, March 2025 GMT

Dubban mutane ne a birnin Amman babban birnin kasar Jordan suka gudanar da zanga-zanga bayan sallar Juma’a domin yin Allah wadai da sake dawo da laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.

A rahoton factjo, dubban mutane sun bayyana goyon bayansu ga al’ummar Gaza a wani gagarumin maci na wannan Juma’a.

Mahalarta tattakin sun yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan masallacin Al-Aqsa a cikin watan Ramadan.

 A cikin wannan maci da aka gudanar bisa gayyatar Harkar Musulunci da kwamitin Tallafawa Falastinawa suka kira, dubban mutane sun halarta da suka hada da wakilai na siyasa, jam’iyyu, da kungiyoyin kwadago, da sauran jama’ar kasa, inda suka yi ta rera taken la’antar ayyukan zalunci na gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, da kuma kin amincewa da duk wata makarkashiyar da aka kulla domin korar Falastinawa daga yankunansu.

Haka nan Wadanda suka halarci tattakin sun yi Allah wadai da kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a zirin Gaza, tare da yin kira ga gwamnatocin kasashen Larabawa da na Musulunci da su dauki matakin gaggawa na dakatar da wannan aika-aikar da Isra’ila ke yi.

Mahalarta tattakin na nuna alhinin shahadar Abu Hamza, kakakin rundunonin Quds Brigade, sun yaba da karfin azamarsa da jajircewarsa, da sadaukar da ransa da jininsa saboda ‘yancin al’ummarsa.

Masu zanga-zangar sun kuma yi Allah wadai da cin amanar Amurkawa, wadanda suka bai wa makiya yahudawan damar soke yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma ci gaba da kashe al’ummar Gaza, tare da bayyana  gwamnatin Amurka a matsayin wadda take daukar nauyin wannan laifi ta hanyar aika bama-bamai da makamai masu linzami ga Isra’ila domin  kisan Falastinawa a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Allah wadai da

এছাড়াও পড়ুন:

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]

Misalan Wannan Hassada:
1. Hassadar Fir’auna a Kan Annabi Musa (AS):
Fir’auna ba ya son aiken da Allah Ya yi wa Annabi Musa (AS) ba, domin yana tsoron cewa mulkinsa zai ƙare. Ya so cewa wannan matsayi na shugabanci da iko ya kasance a gare shi kawai.

Allah Ta’ala Ya ce:” Fir’auna kuma ya ce: ‘Ku bar ni in kashe Musa, kuma ya je ya kira Ubangijinsa! Lallai ni ina tsoron ya canza addininku, ko kuma ya bayyana ɓarna a cikin ƙasa.'” Suratu Gãfir aya ta 26.

Fir’auna bai so wani ya sami iko ko shugabanci sai shi, don haka ya so ya kashe annabi Musa (AS) domin mulkinsa ya dore.

2. Hassadar Ƙuraishawa ga Annabi Muhammad (SAW):
A lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana da’awarsa, manyan shugabannin Ƙuraishawa sun ji haushin hakan, domin suna son a ce su ne kawai suka mallaki wannan matsayi na shugabanci da daraja. Allah Ta’ala Yana cewa “ Yanzu su ne suke raba rahamar Ubangijinka (ta annabi)? Mu ne muka raba musu arziƙinsu a rayuwar duniya. Mu muka ɗaukaka darjojin sashinsu a kan sashi, don wani sashi ya riƙi wani sashi mai yi masa hidima. Rahamar Ubangijinka kuma ita ta fi abin da suke tarawa na duniya.” Suratuz-Zukhruf aya ta 32.

Illolin Wannan Hassada:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Mutum mai irin wannan hassada yana ƙin yarda Allah Ya raba ni’imomi. Yana jin cewa shi ya fi cancanta da wata ni’ima fiye da wanda yake da ita. Wannan yana nuni da ƙarancin imani.

Haddasa Gaba da Rikici: Wannan nau’in hassada yana jawo matsaloli a cikin zamantakewa. Idan mutum yana da burin hana wasu cin gajiyar ni’imar da Allah Ya ba su, to hakan yana haifar da gaba, kishi, da yaƙe-yaƙe a cikin al’umma.

Rashin Albarka a Rayuwa: Allah Ba ya albarkantar da wanda yake da zuciyar hassada. Mutumin da yake son ya hana wani alheri don shi ya mallake shi, sau da yawa ba zai kai ga hakan ba, kuma ko da ya samu, ba zai sami albarka a ciki ba.

Ruɗewa da Rashin Hankali: Mai irin wannan hassadar baya samun kwanciyar hankali. Yana jin kishi da tsananin damuwa idan wani yana cikin ni’ima. Wannan yana iya haifar da ciwon zuciya, matsanancin damuwa, da rashin kwanciyar hankali da nutsuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • Iran da Masar sun tattauna kan rikicin da Isra’ila ta jefa yankin gabas ta tsakiya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet