Wani Sufeto Dansandan da ke aiki a Jihar Kuros Ribas, ya harbe matar abokin aikinsa har lahira tare da jikkata wasu mutane biyu a harbe-harben da ya yi a ranar Lahadi.

Mai magana da yawun rundunar, SP Irene Ugbo, ta tabbatar da faruwar lamarin ga Labarai a birnin Kalaba, inda ta bayyana cewa jami’an Dansandan ya nuna halayyar da ba ta dace ba kafin ya fara harbe-harben.

Ba Na Goyon Bayan Dakatar Da Gwamnan Jihar Ribas – Ndume Bututun Iskar Gas Ya Sake Fashewa A Ribas

Ugbo, ta ƙara da cewa jami’in, naaiki ne a Cibiyar ‘Yansanda ta Atakpa, ya dawo daga aikin dare a wani bankin ‘Microfinance’ kafin afkuwar lamarin. Ta kuma bayyana cewa tuni an kama wanda ake zargi, inda su kuma waɗanda suka jikkata ke samun kulawar likitoci a asibiti.

Bincike ya nuna cewa ɗansandan ya fara nuna alamun taɓun hankali tun bayan dawowarsa daga aikin dare, inda ya rufe ƙofar shiga ofishin ‘yansandan tare da hana kowa fita ko shigowa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani

Samira Sani ‘yar asalin garin Kano ne da ta shigo Masana’anrtar Kannywood a 2022.

A tattaunarta da Aminiya, ta ba da tarihinta da kuma yadda ta daɗe tana mu’amala da ‘yan Kannywood kafin ta fara fitowa a fim:

Za mu so ki gabatar da kanki?

Suna na Samira Sani, jaruma a Masanartar Fim ta Kannywood.

Mene ne tarihinki a takaice?

To ni ‘yar asalin garin Kano ne. An haife ni a garin Dakatsalle da ke Karamar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano.

Na yi makarantun firamare da sakandare duk a Dakatsalle, bayan na gama sakandare sai aka yi min aure, daga baya Allah Ya kawo ni cikin birnin Kano.

Ke nan kin taɓa yin aure?

Eh na taɓa yin aure, kuma ina da ‘ya’ya uku.

Ta yaya kika samu kanki a Kannywood?

Ta sanadiyyar wata ƙawata, wacce take ‘yar fim ce, tana gayyata ta, muna zuwa wurin daukar fim, a hankali a hankali, ‘yan Kannywood suka san ni, ni ma na san mutane.

A wace shekara kika shiga Kannywood?

Na shiga ne a shekara 2022, shekaru uku ke nan, amma ban fara fitowa a fim ba sai a shekarar 2023.

Me ya ba ki sha’awa kika shiga Kannywood?

A da gaskiya ba na sha’awar Kannywood.

Saboda me?

Saboda yadda ake zagin ‘yan fim, ana cewa ‘yan iska ne, to sakamakon na shiga cikinsu, na ga irin yadda suke da mu’amala mai kyau, suna son junansu, domin idan na je ana daukar fim, za ka ga ana wasa da dariya, har sai ka ji ba ka son rabuwa da su.

To a haka sai na fuskanci abin da ake faɗa a kan ‘yan fim ba gaskiya ba ne, wasu ne suke masa kallo a baibai.

To daga nan sai na ji ina sha’awar abin, to sai na fahimtar da iyayena da ‘yan’uwana, To a haka na shiga Kannywood, inda na fara a hannun Darakta Mujahid M. Soja.

To ke nan sai da kika fara mu’amala da ‘yan Kannywood sannan kika fara fim da su haka ne?

Kwarai kuwa, sai da na fara mu’amala da su sannan na shiga Kannywood, saboda a gaskiya a da ina dari-dari da shiga fim, ina gudun kar a ce mini ‘yar iska to amma da na yi mu’amala da su, sai na fahimce su, kuma na ga abin da ake yi a waje ba a yin sa a fim.

Domin ina mu’amala da ‘yan fim ina yi da wadanda ba ‘yan fim ba, shekara biyu ina mu’amala da ‘yan fim sannan na fara.

To da wane fim kika fara?

Na fara da wata waƙa ce mai suna Ladidi mai Koko da Sosai, wacce muka yi da dan Yarbawa da Kamal Aboki (marigayi) da Adam Dorayi.

A ɓangaren fim kuwa na fara da fim din ‘Yar Tiktok na Darakta Mujahid M. Soja.

Ya zuwa yanzu finafinai nawa ne kika yi?

Za su kai 8 zuwa 9, wadanda suka haɗa da: ‘Yan Tiktok da Soyayya Daya da Buri da Niniya da Umarni da kuma Jikokin Mai gari da sauransu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Bututun Iskar Gas Ya Sake Fashewa A Ribas
  • Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola
  • An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara 
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno