Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum
Published: 24th, March 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya jaddada kudirin gwamnatinsa na sake farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu da aka daɗe da watsi da ita domin bunƙasa noman rani da nufin samar da wadataccen abinci a Kudancin Borno da ma Jihar ta Borno gaba ɗaya.
Zulum ya yi wannan alkawarin ne a yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa Mai martaba Sarkin Biu, Mustapha Umar Mustapha, a ziyarar aiki ta kwana uku da ya kai masarautar kwanakin baya.
“Kokarin farfado da wannan madatsar ruwa na da matuƙar muhimmanci wajen magance ƙalubalen ƙarancin ruwa da aka shafe shekaru biyu ana yi a yankin,” in ji gwamnan.
Ya kuma jaddada cewa, farfado da madatsar ruwan zai dawo da ayyukan noman rani masu yawa a Kogin Hawul, wanda zai amfanar da kananan hukumomi shida na Kudancin Borno.
Da yake jaddada muhimmancin noman rani ga al’umma, gwamnan ya lura cewa, noma ya kasance ginshiƙin manufofin gwamnatinsa, wadda ya ce ita ce manufarsu, domin tabbatar da wadatar abinci da samar da rayuwa mai dorewa, musamman ga wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.
Ya kuma tabbatar wa mai martaba sarki da al’ummar Biu cewa, in an kammala madatsar ruwan a 2026 in Allah Ya so, zai kawo sauyi sosai a fannin noma da kuma damar bunkasa tattalin arziki a yankin.
“Aikin noma na daya daga cikin manyan ginshikan gwamnatina, kuma za mu ci gaba da saka hannun jari a fannin don inganta samar da abinci da inganta rayuwar al’ummarmu,” in ji shi.
Gwamna Zulum ya kuma bayyana cewa, za a kara aiwatar da ayyukan raya kasa a masarautar kafin wa’adinsa ya kare a 2027.
Ya kuma jaddada bukatar hadin kan shugabannin siyasa, inda ya bayyana cewa hadin kai zai iya kara habaka tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa a fadin jihar.
“Abin farin ciki ne ganin cewa Jihar Borno ba ta fama da rikicin siyasa, ‘yan majalisar dokokinmu na kasa da na jiha da sauran masu rike da mukaman siyasa, sun ci gaba da kasancewa da haɗin kai wajen samar da ribar dimokuraɗiyya,” in ji Zulum.
A nasa martanin, Mai martaba Sarkin Biu Mustapha Umar Mustapha ya yaba wa Gwamna Zulum bisa jajircewarsa wajen gudanar da ayyukan da suka shafi al’umma a Masarautar Biu.
Ya kuma yaba wa gwamnan musamman kan kaddamar da shirin tallafa wa matasa da marasa galihu, wadanda rikicin shekaru 15 na masu ta da kayar baya da aka yi fama da shi a Jihar Borno da ma wasu jihohin makwabta ya shafi rayuwarsu.
Sarkin ya nuna jin dadinsa da tallafin da gwamnatin jihar ke ci gaba da bai wa al’ummar jihar, inda ya tabbatar da cewa, shirin farfado da madatsar ruwa ta Biu da sauran ayyukan raya kasa za su inganta rayuwar mazauna yankin.
Kasancewar noma a sahun gaba a cikin abubuwan da gwamnatinsa ta sa gaba, ana sa ran sake mayar da hankali kan noman rani da Gwamna Zulum ya yi alkawarin zai bunkasa domin inganta tattalin arziki da kuma karfafa juriyar al’ummar Borno kan karancin abinci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum jihar Borno Madatsar Ruwa Noman rani da madatsar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.
Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.