Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
Published: 24th, March 2025 GMT
Aƙalla fursunoni 12 ne suka tsere baya sun fasa wani gidan yari da ke garin Kotonkarfe a Jihar Kogi.
Kwamishinan watsa labarai na jihar, Kingsley Fanwo ya tabbatar da aukuwar lamarin.
Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a SaudiyyaMista Fanwo ya ƙara da cewa tuni sun sake kama fursuna ɗaya daga cikin waɗanda suke tsere ɗin.
Gwamnatin Kogi ta ce za ta haɗa ƙarfi da ƙarfe da jami’an tsaro domin gano yadda fursunonin suka samu nasarar tserewa a safiyar ranar Litinin.
Kwamishinan ya bayyana lamarin da abin takaici, “sannan yadda fursunonin suka iya tserewa ba tare da barin wata alama ba abin tambaya ne.
“Dole a gudanar da bincike mai zurfi, sannan a kamo fursunonin da suka tsere, sannan a gano waɗanda suke da hannu,” in ji Fanwo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yari Jihar Kogi
এছাড়াও পড়ুন:
ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
Wannan ya taimaka wajen kawo ƙarshen yaƙin basasa a Laberiya da Saliyo.
Duk da haka, ƙungiyar ta fuskanci ƙalubale, musamman bayan juyin mulki a ƙasashen Mali, Burkina Faso, da Nijar a cikin shekarun baya-bayan nan.
Shin ECOWAS na iya ci gaba da aiwatar da ayyukanta kamar da?Sai dai har yanzu wasu na yi wa ƙungiyar kallon hadarin kaji, kan zargin ta gaza cimma wasu muradu da aka kafa ta a kai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp