NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
Published: 24th, March 2025 GMT
Hukumar yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta kama wata mata ‘yar ƙasar Indiya mai suna Neetu Neetu, mai shekara 42, a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano, ɗauke da hodar iblis mai nauyin kilo 11 da aka ɓoye a cikin ledojin da ke kama da kwallon alawar cakulati. An cafke ta ne a yayin binciken shigowarta daga jirgin Qatar Airways daga Bangkok ta Vietnam da Doha.
Shugaban hukumar, Birgediya Janar Buba Marwa (Rtd), ya ce wannan kamun ya sake nuna yadda masu safarar kwayoyi ke amfani da ‘yan ƙasashen waje don kutsawa da miyagun kwayoyi cikin ƙasar. A cewarsa, NDLEA na ci gaba da daƙile irin wannan yunƙuri ta hanyar bayanan sirri da fasahohin zamani.
NDLEA Ta Gargadi Iyaye Kan Bayyanar Alawar Ƙwaya A Kano Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe SuA wani sumame a Kano, an kama Michael Ogundele dauke da tramadol guda 50,000 da aka boye a cikin bututun gas, yayin da a Gunduwawa aka cafke Sunday Ogar da kilogram 27 na wiwi. Haka zalika, an kama Khadijah Abdullahi a Lungun Bulala da kwalabe 424 na maganin tari mai sinadarin Kodin.
A Lagos kuwa, jami’an NDLEA sun kama mutane da dama da wiwi, da tramadol, da Kodin a Mushin, Apapa da Ikotun. NDLEA ta ci gaba da shirinta na wayar da kai a faɗin ƙasar, ciki har da makarantu da masallatai. Marwa ya yaba wa jajircewar jami’an hukumar, yana mai kira da su ci gaba da aiki da kwazo da rikon amana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
Wani matashi ɗan shekara 18 mai suna Bakura Muhammed, ya gamu da ajalinsa a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin matasa masu gaba da juna da ake wa laƙabi da Malians a Maiduguri.
Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zaga-zola Makama cewa, rikicin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar 4 ga watan Afrilun nan a yankin Ajari da Tashar Lara, inda matasan ɓangarorin biyu suka yi artabu da juna.
An daɓa wa wanda aka kashen wuƙa a ciki, wanda ba tare da ɓata lokaci ba jami’an tsaro na Maidugurin suka ɗauke shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.
Wata majiyar ‘yan sanda ta ce, an kama wasu mutane bakwai masu shekaru tsakanin 15 zuwa 24.
Majiyar ta bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Ba’abba Kyari mai kimanin shekara 20 sai Ali Alhaji Goni Ali dan shekara 20 da Muhammed Audu mai kimanin shekara 18, sai Ali Isa mai shekara 15 da Adam Sabir mai shekara 15 da Mohammed Tujja shekaru 17 da Usman Kasim dan shekara 24