Aminiya:
2025-04-15@11:37:36 GMT

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Published: 24th, March 2025 GMT

Wasu daga cikin gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP sun maka Shugaba Bola Tinubu a Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara.

Gwamnonin sun garzaya kotun ne domin neman fatawa game da abin da sashe na 305 na kundin mulkin ƙasar ke nufi.

Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta

Gwamnonin da ke kan gaba a shigar da ƙarar sun haɗa da na jihohin Adamawa, Bauchi, Bayelsa, Enugu, Osun, Filato, Zamfara.

Daga cikin abubuwan da suke nema akwai neman kotun ta ɗauki matsaya kan ko sashen na 305 na kudin mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa shugaban ƙasa dama ya dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da mataimakiyarsa da majalisar dokoki ta jiha, kuma ya naɗa wani gwamnan riƙo a ƙarƙashin dokar ta-ɓaci.

A ƙunshin takardun da suka gabatar wa kotun, gwamnonin sun ce dakatar da zaɓaɓɓun shugabanni da Shugaba Tinubu ya yi na cin karo da sassa na 1(2) da na 5(2) da kuma na 305 da ke ƙunshe a Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya.

Matakin na zuwa bayan huɗu cikin shida na gwamnonin yankin kudu maso kudu sun yi tir da dokar da Tinubu ya ayyana a Ribas.

Gwamnan Bayelsa Duoye Diri, wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin, ya ce, “rikicin siyasar na Ribas bai kai abin da za a ayyana dokar ta-ɓaci a kai ba kamar yadda sashe na 305(3) ya tanada.”

Sai dai kuma, gwamnonin Edo da na Kuros Riba sun goyi bayan matakin na Shugaba Tinubu.

A gefe guda kuma, ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Socio-Economic Rights and Accountability Project (Serap) ta ce ta shigar da Tinubu ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja game da dakatar da gwamnan Ribas da mataimakiyarsa da majalisar dokoki “wanda ya saɓa wa doka”.

Ana iya tuna cewa, a ranar 18 ga wannan wata na Maris ne Tinubu ya dakatar da Gwamna Similanayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da duk ’yan majalisar dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida tare da ɗora tsohon Babban Hafsan Sojin Ruwa, Rear Admiral Ibok-Ete Ibas a matsayin kamtoman jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnoni Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

 Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12

Gwamnatin kasar Ajeriya ta bayyana jami’an diflomasiyyar Faransa da suke kasar su 12 a matsayin ‘wadanda ba a bukatar ganinsu” a cikin kasar, tare da yin kira a gare su da su fice a cikin sa’oi 48.

Bugu da kari kasar ta Aljeriya ta yi suka da kakkausar murya akan ministan harkokin wajen Faransa Bruno Rotayo,tare da cewa za ta mayar masa da martanin da ya dace.

Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Aljeriya ta bayyana cewa; A matsayinta na kasa mai cikakken shugabanci, tana daukar ma’aikatan ofishin jakadanci Faransa 12 a matsayin wadanda ba a maraba da su, sannan kuma ana bukatar da su fice daga kasar a cikin sa’oi 48.”

 Aljeriya din ta dauki wannan matakin ne a matsayin mayar da martani ga kama wani jami’in diflomasiyyarta da aka yi a kasar Faransa a ranar 8 ga watan Aprilu da ake ciki.

Aljeriyan ta bayyana abinda ya faru da cewa, keta hurumin kasarta ne da kuma take dokokin aikin diflomasiyya.”

Haka nan kuma ta yi ishar da cewa, ma’aikacin diflomasiyyar da aka kama yana da kariya ta aiki wacce ta hana a yi masa abinda ya faru,amma kuma gwamnatin Faransa ta yi mu’amala a shi ta hanya mafi muni da halayya irin ta barayi.’

Alaka a tsakanin Faransa da Aljeriya tana kwan-gaba da baya, musamman a cikin watannin bayan nan. Watanni 8 da su ka gabata an sami rashin jituwa a tsakaninsu saboda korar wasu ‘yan asalin Aljeriya mazauna Faransa bisa zargin cewa sun shiga kasar ba bisa ka’ida ba. Aljeriya ta yi wa jakadanta kiranye, tare da rufe kafar diflomasiyya a tsakaninsu na tsawon watanni 8.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
  • Yaƙin Neman Zaɓe A 2027: Ƙungiya Ta Nemi A Maye Gurbin Mai Magana Da Yawun Shugaban Ƙasa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu