Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
Published: 24th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Iran tana cikin shirin ko-ta-kwana akan duk wani abu da zai iya bijirowa, kuma a halin yanzu ba batun yaki ake yi ba.
A wata ganawa da ministan harkokin wajen na Iran ya yi da tawagar kungiyar agaji ta “Red Cross” a karkashin jagorancin shugabanta Koliband, ministan harkokin wajen na Iran ya yabawa aikin nasu, tare da cewa; Duk da cewa ana cikin lokacin hutu, amma su a kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana domin gabatar da ayyukan agaji da hakan yake nuni da yi wa al’umma hidima ta koli.
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kuma ce: Su ma sojoji da jami’an tsaro kamar ku suke aiki, ba su da lokacin hutu,kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana.
Haka nan kuma ya kara da cewa; Kowane bangare na gwamnati yana cikin shirin ko-ta-kwana domin fuskantar kowane irin yanayi.
Har ila yau, babban jami’in diflomasiyyar ta Iran ya ce; Ina da tabbacin cewa babu wani mahaluki da yake tunanin kawo wa Iran hari, domin suna sane da sakamakon da take tattare da yin hakan, sun kuma san cewa kowane bangare na gwamnati yana cikin shiri.
Abbas Arakci ya kuma bayyana cewa baya ga ayyukan agaji da kungiyar take yi a cikin gida, tana kuma gabatar da wasu ayyukan na taimako a kasashen waje. Ya kuma yi ishara da lokacin girgizar kasar Japan, da hukumar agaji ta Iran ta kai dauki, wanda ya taka rawa wajen kara bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
UNRWA : hana shigar da kayan agaji Gaza, ya jefa yankin cikin matsanancin hali
Shugaban hukumar kula da ‘yan gudun hijira falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA) ya yi gargadin cewa hana shigar da kayayyakin jin kai da Isra’ila ta yi a zirin Gaza ya jefa yankin cikin mawuyacin hali na rashin abinci.
“Makonni uku kenan da hukumomin Isra’ila suka hana shigar da kayayyaki cikin Gaza.
“Ba abinci, ba magani, ba ruwa, babu man fetur,” inji Philippe Lazzarini a cikin wani sako a shafukan sada zumunta.
Tun a ranar 4 ga watan Maris ne Isra’ila ta hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza, bayan karewar kashi na farko na tsagaita bude wuta a yarjejeniyar da ta cimma da kungiyar gwagwarmayar falasdianwa ta Hamas data kunshi musayar fursunoni tsakanin bangarorin.
Lazzarini ya jaddada cewa al’ummar Gaza sun dogara ne kan shigo da kayayyaki daga yankunan da aka mamaye.
“Duk ranar da ta wuce ba tare da agajin jin kai ba, hakan na nufin yara da yawa suna kwana da yunwa, cututtuka na yaduwa,” in ji babban jami’in UNRWA.
Lazzarini ya bayyana haramcin taimakon a matsayin wani hukuncin bai daya ga al’ummar Gaza, wadanda akasarinsu kananan yara ne da mata.
Ya yi kira da a dage wannan kawanya da kuma kai agajin jin kai da kayayyakin kasuwanci zuwa Gaza.