Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
Published: 24th, March 2025 GMT
Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Barri ya jaddada cewa; HKI tana kokarin jefa Lebanon cikin tarkon kulla alaka da ita, yana mai jaddada cewa; Ko kadan Lebanon ba ta kama wannan hanyar ba.
Nabih Barri ya bayyana yadda wasu rahotanni daban-daban suke Magana akan cewa Amurka tana kai gwauro da mari, domin ganin an bude alaka kai tsaye a tsakanin Lebanon da HKI.
Shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya ce, ko kadan kasar Lebanon ba ta tunanin kulla alaka da HKI.
Haka nan kuma ya yi ishara da tsagaita wutar yaki wacce a kodayaushe HKI take ketawa, yana mai tabbatar da cewa Hizbullah tana riko da ita, don haka ya yi kira ga Amurka da sauran bangarorin da suke a cikin tsagaita wutar da su yi matsin lamba ga HKI domin ta yi aiki da ita.
Bugu da kari Nabih Barri ya ce; Sojojin kasar ta Lebanon sun gama shiryawa domin shiga cikin kudancin tafkin Laitani, amma matsalar da ake fuskanta ita ce yadda Isra’ila take kin janyewa daga wasu yankuna a cikin Lebanon.
Nabih Barri ya kuma jaddada cewa; Kungiyar Hizbullah tana aiki da tsagaita wutar yakin, kuma ba ta keta ta ba ko kadan.
Shugaban Majalisar Dokokin kasar ta Lebanon ya kara da cewa; Duk da cewa HKI tana keta tsagaita wutar yaki, amma ko sau daya Hizbullah ba ta harba ko harsashi daya ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tsagaita wutar
এছাড়াও পড়ুন:
Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
A kwanan nan ne sakatare janar na kungiyar ASEAN Kao Kim Hourn ya bayyana a wata hirar da ya yi da wakilin babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, nasarorin da Sin ta samu ta fuskar ci gaba ba sakamakon ‘siddabaru’ ba ne, illa sakamakon aiki tukuru kuma mai dorewa.
Kao Kim Hourn, wanda ya ziyarci kasar Sin sau da dama, ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a wadannan ziyarce-ziyarcensa. Ya bayyana cewa, tafiya daga filin jirgin sama zuwa tsakiyar gari, ya shaida yadda kasar Sin take da tsabta, da koren muhalli, da tsaro, da duk sakamakon ci gabanta na zahiri. Abin ban mamaki ne ganin yadda kasar Sin ta canza a cikin ‘yan shekarun nan. Abubuwan da ya gani a kasar Sin a cikin ‘yan shekarun nan sun matukar bambanta da abubuwan da ya gani lokacin da ya ziyarci kasar Sin a shekarun 1990.
Ya jaddada cewa, irin wadannan sauye-sauyen na nuna gagarumin kokari na bayan fage. Kana samun ci gaba yana bukatar aiki tukuru. Kao ya bayyana cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ne ba ta hanyar siddabaru ba, ta samu ne a sakamakon namijin kokarin da shugabannin kasar Sin da jama’arta suka yi. Ya kuma kara da cewa, ci gaban kasa yana bukatar kuzari mai yawa, da nagartaccen jagoranci, da dimbin albarkatu, da jajircewar al’ummarta. Kasar Sin misali ce ga hakan. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp