HausaTv:
2025-03-25@21:04:44 GMT

Harin Neman Shahada Ya Kashe ‘Dan Share Wuri Zauna Daya A Garin Haifa

Published: 24th, March 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa; An kai hari nau’i biyu, da ya hada amfani da motar take mutane da kuma bude wuta daga bindiga. Harin da aka kai a kusa da yankin “Yukna’am Iliyat” dake gabashin garin Haifa, ya yi sanadiyyar halakar wani dan share wuri zauna da kuma jikkata wani guda daya.

‘Yan sandan HKI sun ambaci cewa, wanda ya kai harin ya isa wurin ne a cikin motarsa, inda ya sami ‘yan share wuri zauna da yawa a tashar mota, ya kuma bude wuta akan masu wucewa da hakan ya yi sanadiyyar jikkata wasu da dama.

Ma’aikatan Agaji kuwa sun amabci cewa baya ga halaka da kuma jikkatar ‘yan share wuri zauna, an harbe mahari.

Tashar talabijin din “Cane” ta ambaci cewa; Wanda ya kai harin Bapalasdine dag acikin yakin yankin Falasdinu dake karkashin mamaya tun 1948.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Wasu daga cikin gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP sun maka Shugaba Bola Tinubu a Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara.

Gwamnonin sun garzaya kotun ne domin neman fatawa game da abin da sashe na 305 na kundin mulkin ƙasar ke nufi.

Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta

Gwamnonin da ke kan gaba a shigar da ƙarar sun haɗa da na jihohin Adamawa, Bauchi, Bayelsa, Enugu, Osun, Filato, Zamfara.

Daga cikin abubuwan da suke nema akwai neman kotun ta ɗauki matsaya kan ko sashen na 305 na kudin mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa shugaban ƙasa dama ya dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da mataimakiyarsa da majalisar dokoki ta jiha, kuma ya naɗa wani gwamnan riƙo a ƙarƙashin dokar ta-ɓaci.

A ƙunshin takardun da suka gabatar wa kotun, gwamnonin sun ce dakatar da zaɓaɓɓun shugabanni da Shugaba Tinubu ya yi na cin karo da sassa na 1(2) da na 5(2) da kuma na 305 da ke ƙunshe a Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya.

Matakin na zuwa bayan huɗu cikin shida na gwamnonin yankin kudu maso kudu sun yi tir da dokar da Tinubu ya ayyana a Ribas.

Gwamnan Bayelsa Duoye Diri, wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin, ya ce, “rikicin siyasar na Ribas bai kai abin da za a ayyana dokar ta-ɓaci a kai ba kamar yadda sashe na 305(3) ya tanada.”

Sai dai kuma, gwamnonin Edo da na Kuros Riba sun goyi bayan matakin na Shugaba Tinubu.

A gefe guda kuma, ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Socio-Economic Rights and Accountability Project (Serap) ta ce ta shigar da Tinubu ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja game da dakatar da gwamnan Ribas da mataimakiyarsa da majalisar dokoki “wanda ya saɓa wa doka”.

Ana iya tuna cewa, a ranar 18 ga wannan wata na Maris ne Tinubu ya dakatar da Gwamna Similanayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da duk ’yan majalisar dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida tare da ɗora tsohon Babban Hafsan Sojin Ruwa, Rear Admiral Ibok-Ete Ibas a matsayin kamtoman jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samu Bunkasa A Fannin Neman Ikon Mallakar Fasaha A Ofishin EPO
  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar