Babban kamfanin fasahar nan na Amurka wato Apple, ya sanar da shirinsa na zuba jarin da ya kai kudin Sin yuan miliyan 720, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 100.31, a fannin samar da makamashi mai tsafta da ake iya sabunta amfani da shi a kasar Sin.

Wata sanarwa da kamfanin ya fitar a Litinin din nan, ta ce kudaden jarin za su samar da damar kara yawan megawatt duk sa’a kusan 550,000 na lantarkin da ake samarwa ta iska, da hasken rana duk shekara, cikin jimillar lantarkin kasar Sin, adadin da kuma ake fatan karuwarsa yayin da masu zuba jari suka karu.

Kazalika, sanarwar ta hakaito babban jami’in gudanarwa na kamfanin Jeff Williams, na cewa yanzu haka masu samarwa kamfanin Apple kayayyakin harhada hajojinsa a kasar Sin na kan gaba wajen samar da ci gaban fasahohi masu nasaba da na’urori masu kwakwalwa, da fannin makamashi mai tsafta.

Williams ya kara da cewa, sakamakon kaddamar da kudaden jarin na wannan karo, kamfanin Apple na fatan kara zurfafa hadin gwiwarsa da sassan masu samar masa da kayayyaki na Sin, ta yadda za a kai ga ingiza kirkire-kirkire domin cin gajiyar dukkanin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa

A cewarsa, domin tabbatar da gudanar da wannan tantancewar, an samar da kwakkwaran kwamitoci a matakin jiha da kananan hukumomi tare da sauran sassan hukumomin da ke da alaka da kudi, sannan an ba su umarni samar da dukkan bayanan biyan albashin nan take.

Farouk ya bukaci ma’aikatan da matsala ta shafa su kai kansu gaban hukumominsu tare da nagartattun bayansu kan dalilin kin bin wannan umarni, saboda a kula da sabunta kundin biyan albashin.

Ya ce Mambobin kwamitin sun hada da manyan sakatarorin daga manyan ma’aikatu, wakilai daga kwamitin tsara jadawalin albashi da kuma wasu manyan jami’an a ofishin sakataren gwamnatin Jihar Kano. Sannan ya jadadda cewa bin wannan umarni ya zama wajibi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanin BYD Ya Samu Karin Ribar Kaso 34 Zuwa Dala Biliyan 5.6 A Bara
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa