Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
Published: 25th, March 2025 GMT
Misalan Wannan Hassada:
1. Hassadar Fir’auna a Kan Annabi Musa (AS):
Fir’auna ba ya son aiken da Allah Ya yi wa Annabi Musa (AS) ba, domin yana tsoron cewa mulkinsa zai ƙare. Ya so cewa wannan matsayi na shugabanci da iko ya kasance a gare shi kawai.
Allah Ta’ala Ya ce:” Fir’auna kuma ya ce: ‘Ku bar ni in kashe Musa, kuma ya je ya kira Ubangijinsa! Lallai ni ina tsoron ya canza addininku, ko kuma ya bayyana ɓarna a cikin ƙasa.
Fir’auna bai so wani ya sami iko ko shugabanci sai shi, don haka ya so ya kashe annabi Musa (AS) domin mulkinsa ya dore.
2. Hassadar Ƙuraishawa ga Annabi Muhammad (SAW):
A lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana da’awarsa, manyan shugabannin Ƙuraishawa sun ji haushin hakan, domin suna son a ce su ne kawai suka mallaki wannan matsayi na shugabanci da daraja. Allah Ta’ala Yana cewa “ Yanzu su ne suke raba rahamar Ubangijinka (ta annabi)? Mu ne muka raba musu arziƙinsu a rayuwar duniya. Mu muka ɗaukaka darjojin sashinsu a kan sashi, don wani sashi ya riƙi wani sashi mai yi masa hidima. Rahamar Ubangijinka kuma ita ta fi abin da suke tarawa na duniya.” Suratuz-Zukhruf aya ta 32.
Illolin Wannan Hassada:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Mutum mai irin wannan hassada yana ƙin yarda Allah Ya raba ni’imomi. Yana jin cewa shi ya fi cancanta da wata ni’ima fiye da wanda yake da ita. Wannan yana nuni da ƙarancin imani.
Haddasa Gaba da Rikici: Wannan nau’in hassada yana jawo matsaloli a cikin zamantakewa. Idan mutum yana da burin hana wasu cin gajiyar ni’imar da Allah Ya ba su, to hakan yana haifar da gaba, kishi, da yaƙe-yaƙe a cikin al’umma.
Rashin Albarka a Rayuwa: Allah Ba ya albarkantar da wanda yake da zuciyar hassada. Mutumin da yake son ya hana wani alheri don shi ya mallake shi, sau da yawa ba zai kai ga hakan ba, kuma ko da ya samu, ba zai sami albarka a ciki ba.
Ruɗewa da Rashin Hankali: Mai irin wannan hassadar baya samun kwanciyar hankali. Yana jin kishi da tsananin damuwa idan wani yana cikin ni’ima. Wannan yana iya haifar da ciwon zuciya, matsanancin damuwa, da rashin kwanciyar hankali da nutsuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo
Wani ɗan ƙasar Turkiyya da ya rasa gidansa sakamakon wata gagarumar girgizar ƙasa a shekarar 2023, ya shafe shekara biyu yana zaune shi kadai a cikin wani ƙaramin kogo saboda yana ganin ya fi kowane gini da mutum zai yi karko.
A watan Fabrairun 2023, Kudancin Turkiyya ya fuskanci ibtila’in girgizar kasa mai karfin 7.8 da ta yi sanadiyyar mutuwar dubun-dubatar mutane tare da mayar da daukacin unguwanni tamkar kufai.
An yi wa wata karya tiyatar ceton rai Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — JonathanAli Bozoğlan, mahaifin ‘ya’ya uku daga lardin Hatay da ke kudancin kasar, ya rasa gidansa sakamakon girgizar kasar da aka yi a ranar 6 ga watan Fabrairu 2023.
Duk da cewa shi da iyalinsa sun tsira ba tare da wata matsala ba, Ali ya firgita da girgizar kasar har ya yanke shawarar ba ya son zama a ginin da mutum ya yi.
Maimakon haka, sai ya sami wani karamin kogo da zai iya zama lafiya a wajen birnin, inda ya mayar da shi gida.
Kodayake ya kasa shawo kan iyalinsa su hadu da shi don zama a cikin kogon da ba a saba gani ba, sai dai ya yi ikirarin cewa yana farin ciki kuma yana cikin kwanciyar hankali a inda yake.
Ali Bozoğlan ya shaida wa kafar yada labarai ta TGRT Haber cewa, “Na shafe shekara 2 ina zaune a nan bayan girgizar kasar kuma na sami kwanciyar hankali a cikin wannan kogon.
“Wannan kogon ya wanzu tsawon dubban shekaru kuma bai rushe ba.”
Bayan da an samu labarin yadda mutumin yake rayuwa, sai Hakimin Defne ya ba shi wata kwantenar gida mai kyau a wani wuri kusa da birnin, amma Ali ya so ya nisantar da kansa da birni mai cike da cunkoson jama’a, domin ya saba da rayuwar kwanciyar hankali a cikin karamin kogon nasa.
“Ina wanke kwanukan abincina da yin wanki da kuma yin abincin da zan ci. Ina yin kyakkyawar rayuwa a cikin kogon,” in ji Ali.
“Ba ni da kowa kuma ina hulda da yanayi. Mutanen da ba su da ilimi suna yin munanan maganganu game da rayuwata a cikin kogon.
“Domin ba sa zama da ni, suna magana da ni, kuma ba su san ni ba, suna yin kalamai daban-daban.”
Ali ya yarda cewa zama shi kadai a cikin kogo bai dace ba. Domin wuri ne mai zafi sosai a lokacin hunturu da sanyi da rani, yana jawo macizai da beraye, amma duk da haka ya saba da shi.
Haka kuma ya so ya sami ya rika shiga bandaki da samun ruwan sha, amma ba zai yiwu ba.
Yanzu ya shirya saka na’urorin samar da lantarki ta hasken rana domin ya iya sarrafa injin wanki da firinjinsa, amma ko da mafarkinsa bai zama gaskiya ba, ba zai yi watsi jin dadin kogon nasa ba.