NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
Published: 25th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Mulkin dimokuraɗiyya kamar yadda Hausawa ke cewa ‘yancin ɗan adam.
A lokacin da ta ba ka damar tsayawa don a zaɓe ka kan wani muƙamin, kazalika ta ba ka damar zaɓen wanda kake so ya shugabance ka kuma ya wakilce ka.
Wani abun da dimokuraɗiyyar ta bai wa al’umma dama a kai kuma shi ne na yin kiranye ga wakilan da suka zaɓa musamman idan waɗannan wakilan basa biya musu buƙatun da suka tura su a kai.
Tuni dai al’ummar Kogi ta Tsakiya suka fara kaɗa ƙuri’un kiranye ga Sanata Natasha da suka aike ga Majalisar Dattawa bisa dalilai nasu na ƙashin kan su.
NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen GwamnaShirin Najeriya A Yau na wannan rana zai tattauna ne kan matakai da sharuɗan da ake cikawa don yin kiranye ga ‘yan majalisa.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Majalisar dattawa kiranye
এছাড়াও পড়ুন:
Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo
Wani ɗan ƙasar Turkiyya da ya rasa gidansa sakamakon wata gagarumar girgizar ƙasa a shekarar 2023, ya shafe shekara biyu yana zaune shi kadai a cikin wani ƙaramin kogo saboda yana ganin ya fi kowane gini da mutum zai yi karko.
A watan Fabrairun 2023, Kudancin Turkiyya ya fuskanci ibtila’in girgizar kasa mai karfin 7.8 da ta yi sanadiyyar mutuwar dubun-dubatar mutane tare da mayar da daukacin unguwanni tamkar kufai.
An yi wa wata karya tiyatar ceton rai Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — JonathanAli Bozoğlan, mahaifin ‘ya’ya uku daga lardin Hatay da ke kudancin kasar, ya rasa gidansa sakamakon girgizar kasar da aka yi a ranar 6 ga watan Fabrairu 2023.
Duk da cewa shi da iyalinsa sun tsira ba tare da wata matsala ba, Ali ya firgita da girgizar kasar har ya yanke shawarar ba ya son zama a ginin da mutum ya yi.
Maimakon haka, sai ya sami wani karamin kogo da zai iya zama lafiya a wajen birnin, inda ya mayar da shi gida.
Kodayake ya kasa shawo kan iyalinsa su hadu da shi don zama a cikin kogon da ba a saba gani ba, sai dai ya yi ikirarin cewa yana farin ciki kuma yana cikin kwanciyar hankali a inda yake.
Ali Bozoğlan ya shaida wa kafar yada labarai ta TGRT Haber cewa, “Na shafe shekara 2 ina zaune a nan bayan girgizar kasar kuma na sami kwanciyar hankali a cikin wannan kogon.
“Wannan kogon ya wanzu tsawon dubban shekaru kuma bai rushe ba.”
Bayan da an samu labarin yadda mutumin yake rayuwa, sai Hakimin Defne ya ba shi wata kwantenar gida mai kyau a wani wuri kusa da birnin, amma Ali ya so ya nisantar da kansa da birni mai cike da cunkoson jama’a, domin ya saba da rayuwar kwanciyar hankali a cikin karamin kogon nasa.
“Ina wanke kwanukan abincina da yin wanki da kuma yin abincin da zan ci. Ina yin kyakkyawar rayuwa a cikin kogon,” in ji Ali.
“Ba ni da kowa kuma ina hulda da yanayi. Mutanen da ba su da ilimi suna yin munanan maganganu game da rayuwata a cikin kogon.
“Domin ba sa zama da ni, suna magana da ni, kuma ba su san ni ba, suna yin kalamai daban-daban.”
Ali ya yarda cewa zama shi kadai a cikin kogo bai dace ba. Domin wuri ne mai zafi sosai a lokacin hunturu da sanyi da rani, yana jawo macizai da beraye, amma duk da haka ya saba da shi.
Haka kuma ya so ya sami ya rika shiga bandaki da samun ruwan sha, amma ba zai yiwu ba.
Yanzu ya shirya saka na’urorin samar da lantarki ta hasken rana domin ya iya sarrafa injin wanki da firinjinsa, amma ko da mafarkinsa bai zama gaskiya ba, ba zai yi watsi jin dadin kogon nasa ba.