HausaTv:
2025-04-15@11:47:06 GMT

Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24

Published: 25th, March 2025 GMT

Rahotanni daga Falasdinu na cewa akalla Falasdinawa 61 ne sukayi shahada a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, in ji ma’aikatar lafiya ta Gaza.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, ma’aikatar ta ce an gano gawarwaki hudu a karkashin baraguzan gini, sannan an kwantar da mutane 134 da suka jikkata a asibiti cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Adadin wadanda suka mutu a zirin Gaza ya kai 50,082, yayin da mutane 113,408 suka samu raunuka tun bayan fara yakin kisan kare dangi na Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Har ila yau, a ranar litinin, sojojin Isra’ila sun kai harin bam a asibitin Nasser, mafi girma a kudancin Gaza, da ke Khan Younis, harin da ma’aikatar ta yi Allah wadai da shi a matsayin “laifi na yaki.”

A ranar 1 ga Maris, bayan karewar kashi na farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta, Isra’ila ta kaurace wa shiga shawarwarin kashi na biyu na yarjejeniyar.

Tun a ranar 18 ga watan Maris ne dai aka sake tada jijiyoyin wuya, lokacin da Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare, lamarin da ya karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya

Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.

Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis