Dakarun Yemen sun kara kai hare-hare goyan bayan Falasdinu
Published: 25th, March 2025 GMT
Dakarun sojin Yaman sun ce sun kara kai hare-hare na nuna kyama ga Isra’ila da Amurka a matsayin nuna goyan baya a kan zirin Gaza.
Kakakin rundunar Yahya Saree ya ce a daren jiya litinin sojojin na Yaman sun kai hari filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion na Isra’ila da makami mai linzami guda biyu da suka hada da Zulfiqar mai gudun tsiya.
Ya kara da cewa hare-haren na goyon bayan Falasdinawa ne a Gaza.
Saree ya yi nuni da cewa, dakarun kasar Yemen sun kuma kai hari kan jirgin yakin Amurka Harry S.
Saree ya ce harin da aka kai kan jiragen ruwan yakin Amurka shi ne irinsa na biyu cikin sa’o’i 24 da suka gabata.
Ya ce an kai harin ne domin mayar da martani ga hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar ta Yemen.
Saree ya kuma jaddada cewa za a ci gaba da gudanar da ayyukan adawa da Isra’ila har sai an daina ta’addancin gwamnatin tare da dage killacewar da aka yi wa Gaza.
A ranar 15 ga Maris, Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama da ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar Yemen 53.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kamata Ya Yi Amurka Ta Kara Kokarin Gyara Kuskurenta
Wasu kafofin yada labarai a duniya na ganin cewa, idan gwamnatin Amurka ta ci gaba da saka shingayen haraji, to sauran kasashe za su maye gurbinta a bangaren samar da hidimomi. Abin da gwamnatin ta yi biris da shi yayin da take kididdigar harajin da za ta kakabawa sauran sassa, har yanzu wannan bangare na shiga gogayyar ciniki.
Bisa bayyanan da aka fitar, Amurka ta dade tana cin rarar kudin ciniki a bangaren ba da hidimomi. Alal misali a shekarar 2024, yawan rarar kudin da ta samu a wannan bangare ya kai dala biliyan 300. Kuma Abin lura shi ne, cinikin hidimomi na matukar dogaro da cinikin kayayyaki. Gibin kudin cinikin da Amurka ta samu a bangaren cinikin kayayyaki da rarar kudin cinikin da ta samu ta fuskar cinikin hidimomi, ya faru ne bayan sauyin salon sana’o’i bisa matakai daban daban, ta yadda suka kasance tagwaye da ba za a iya raba su ba.
Idan an yi waiwaye kan tushen cinikin hidimomi wato batun amincewa, a wadannan shekaru da suka gabata, Amurka ta rika sanya takunkumai da haifar da barazana ga dukkanin fadin duniya, wanda hakan ya rage kimarta, da amincewa daga sauran kasashe. A halin yanzu, Amurka ta kakabawa sauran kasashe harajin kwastam yadda take so, kuma abun tambaya shi ne wa zai karbi hidimomin da Amurka za ta samar a bangaren hada-hadar kudi, da ba da ilmi da bayanai da kuma kwamfuta?
Amurka ita kanta za ta dau laifin gogayyar ciniki, matakin da ta dauka a wannan karo na kawar da harajin kwastam na ramuwar gayya kan wasu kayayyaki, dabara ce ta kubutar da kanta daga mawuyacin hali. Amma, hakan bai wadatar ba, dole ne ta dauki karin matakai na soke dukkanin wannan haraji da ta kakabawa sauran kasashe. A wani bangare kuwa, ta mutunta abokan cinikinta, ta yi shawarwari da su bisa adalci da daidaito, a matsayin hanya daya tilo mafi dacewa da za ta bi wajen warware bambancin ra’ayi na ciniki. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp