Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
Published: 25th, March 2025 GMT
Wasu lauyoyi 77 a Jamus sun bukaci gwamnatin kasar da ta mutunta sammacin kotun hukunta manya laifuka ta duniya ICC, na cafke firaministan Isra’ila Banjamin Netanyahu.
A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da da suka fitar, fitattun lauyoyin 77 sun kuma bayyana yiwuwar kasancewar Netanyahu a Jamus a matsayin take doka da kuma hakkin kasar.
Lauyoyin sun soki Friedrich Martin Josef Merz, dan siyasa kuma shugaban gwamnati a nan gaba, saboda sanarwar da ya yi a lokacin yakin neman zabe cewa zai samo hanyar gayyatar firaministan Isra’ila da kuma tattaunawa ta wayar tarho da Netanyahu bayan nasararsa.
Lauyoyin sun kuma yi Allah wadai da halin wasu jami’o’in da suka soke jawabin da Francesca Albanese mai kula da harkokin kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi a yankin Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
Haka zalika, Kangye ya kuma tabbatar wa da al’umma cewa; jami’an tsaro na ci gaba da mayar da hankali wajen cafke fitaccen shugaban ‘yan ta’addan nan, Bello Turji.
Sannan, ya yi watsi da ikrarin da sojoji suka yi na cewa; sun dakile hare-haren makiyaya da ‘yan ta’adda da kuma barayin shanu da sauran makamantansu.
Da yake yin jawabi game da kyautata wa sojojin da suka jikkata, Kangye ya musanta zargin yin watsi da sojojin da suka samu raunuka.
Ya ce, “To, a iya sanina dangane da abin da hukumar sojoji ke yi, sojojinmu na samun isasshiyar kulawa, kuma kai dan jarida ne, da ka lura da lokacin hutun Sallah, za ka ga yadda babban hafsan soji da hafsan hafsoshin sojin sama da wasu manyan hafsoshi daga hedikwatar hukumar suka ziyarci sojojin, domin taya su murnar Sallah.
“Sannan kuma, zan iya fada muku cewa; hedikwatar rundunar sojojin Nijeriya, na kula da marasa lafiya da wadanda suka samu raunuka da wasu da ke bukatar a fitar da su zuwa kasashen waje, ana fitar da su, domin nema musu lafiya; wasu sun tafi Masar, wasu Turkiyya, wasu kuma Kasar Indiya. Kamar yadda muke magana yanzu, wasu har yanzu suna can suna samun kulawar likitoci a can.”
Ya kuma bayyana cewa, a ‘yan watannin da suka gabata, an raba wa sojojin da suka samu jikkata a fagen-daga gidaje.
Kangye ya kuma yi nuni da cewa, an raba wa sojojin da suka jikkatan gidajen kyauta ne, domin kuwa wasu daga cikinsu; ba za su iya dawowa fagen aiki ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp