Kungiyar gwagwarmayar falasdinawa ta Hamas, ta bayyana cewa Isra’ila ta yi amfani da sulhun da aka cimma wajen tattara bayanai kan shugabannin kungiyar ta bi tana kashe su.

Saidai mai magana da yawun kungiyar ya ce kungiyar tana da tushe sosai a Falasdinu wanda kisan gillar da Isra’ila ke yi wa shugabanninta ba, bai zai rusa ta ba.

Sami Abu Zuhri ya bayyana hakan ne bayan da Isra’ila ta kashe wasu jami’an ofishin siyasa na kungiyar ta Hamas guda hudu cikin kasa da mako guda tun bayan da ta koma yakin kisan kare dangi a zirin Gaza, wanda hakan ya saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni biyu da Hamas.

Jinin shugabanni da kwamandojin Hamas iri daya ne da na yara da matasa na Gaza, kuma wadannan kashe-kashen ba za su hana mu ci gaba da gwagwarmaya ba.

Kakakin na Hamas ya kuma nuna rashin jin dadin yadda Isra’ila ke aiwatar da hukuncin kisa a kullum a yankin da aka yi wa kawanya.

“Abin da ke faruwa a Gaza a yanzu ya fi yakin kisan kare dangi da aka shafe watanni 15 ana yi,” in ji shi.

Rahotanni na baya-bayan nan na cewa, akalla Falasdinawa 23 da suka hada da kananan yara bakwai ne aka kashe a hare-haren da Isra’ila ta kai da kafin wayewar gari a wannan Talata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da Isra ila Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

 Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari

 Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Iran tana cikin shirin ko-ta-kwana akan duk wani abu da zai iya bijirowa, kuma a halin yanzu ba batun yaki ake yi ba.

A wata ganawa da ministan harkokin wajen na Iran ya yi da tawagar kungiyar agaji ta “Red Cross” a karkashin jagorancin shugabanta Koliband, ministan harkokin wajen na Iran ya yabawa aikin nasu, tare da cewa; Duk da cewa ana cikin lokacin hutu, amma su a kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana domin gabatar da ayyukan agaji da hakan yake nuni da yi wa al’umma hidima ta koli.

Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kuma ce: Su ma sojoji da jami’an tsaro kamar ku suke aiki, ba su da lokacin hutu,kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana.

Haka nan kuma ya kara da cewa; Kowane bangare na gwamnati yana cikin shirin ko-ta-kwana domin fuskantar kowane irin yanayi.

Har ila yau, babban jami’in diflomasiyyar ta Iran ya ce; Ina da tabbacin cewa babu wani mahaluki da yake tunanin kawo wa Iran hari, domin suna sane da sakamakon da take tattare da yin hakan, sun kuma san cewa kowane bangare na gwamnati yana cikin shiri.

Abbas Arakci ya kuma bayyana cewa baya ga ayyukan agaji da kungiyar take yi a cikin gida, tana kuma gabatar da wasu ayyukan na taimako a kasashen waje. Ya kuma yi ishara da lokacin girgizar kasar Japan, da hukumar agaji ta Iran ta kai dauki, wanda ya taka rawa wajen kara bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban