Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
Published: 25th, March 2025 GMT
Sai dai, tabbas za a karya tsarin, ganin yadda ba a samun adalci a ciki. Mun san kasar Sin daya ce daga cikin kasashen da suka warware dabaibayin hana ci gaba da kasashen yamma suka daura musu, inda ta raya tattalin arzikinta, tare da taka muhimmiyar rawa a cikin tsarin duniya ta fuskar samar da kayayyaki.
Daga bisani me kasar Sin ta yi? Ta samar da tunanin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, inda aka nanata bukatar ba sauran mutane damar jin dadin zaman rayuwa, matukar wani mahaluki na son samun zaman rayuwa mai inganci. Bisa wannan tunani ne, kasar Sin ta samar da jerin shawarwari masu alaka da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar mabambantan al’adu a duniya, da tsayawa kan manufofin tattaunawa tare, da gudanar da aikin gini tare, da raba moriya, gami da sanya kowa a turbar samun biyan bukata, ta yadda kasar ke ta samun amincewa da goyon baya daga karin kasashe.
Tunanin al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, da manhajojin AI na “open source”, duk sabbin dabarun daidaita al’amura ne. A lokacin da wani tsohon abu ya gaza biyan bukata, ya kamata a gwada wani na sabo. Ko ba haka ba?(Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Amnesty Ta Zargi Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ” Amnesty International” ta bayyana cewa, rundunar kai daukin gaggawa ta “RSF” ta bautar da mata da kuma cin zarafinsu.
Kungiyar ta yi tir da abinda rundunar ta “RSF” ta yi akan mata da su ka manyanta da kuma ‘yan mata a tsawon lokacin yakin na Sudan da har yanzu bai zo karshe ba.
Wani sashe na rahoton kungiyar ya yi ishara da yadda wannan rundunar da take fada da sojojin kasar Sudan ta tarwatsa mutane daga gidaje da matsugunansu a fadin kasar.
Ita kuwa Hukumar dake kula da ‘yan gudun hijira ta MDD ( UNHCR) cewa ta yi da akwai yan kasar ta Sudan fiye da 100,000 da suke neman yin hijira zuwa kasashen turai a cikin wannan shekara ta 2025 kadai, tare da kara da cewa mutanen suna kara yanke kauna da samun wata mafita a cikin kasar, saboda raguwar agaji.
A cikin birnin Khartum da sojojin su ka kori dakarun na “RSF” an sami komawar mutanen da su ka yi hijira kamar yadda hukumar ta ( UNHCR) ta ambata.
Shugabar hukumar mai kula da ‘yan hijira ta MDD Olga Sarado wace ta gudanar da taron manema labaru a birnin Geneva ta bayyana cewa; Da akwai ‘yan Sudan su 484 da su ka isa cikin kasashen turai daga watan Janairu zuwa yanzu, da hakan yake nuni da samun Karin masu hijirar zuwa turai da kaso38%.
Ta kuma kara da cewa, matukar ba a kai wa kasar kayan agaji, to kuma masu yin hijira zuwa turai din zai karu.