An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Kan Karfafa Rawar Da MDD Ke Takawa A Beijing
Published: 25th, March 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ya ce a jiya Litinin, ma’aikatar harkokin wajen Sin ta gudanar da taron karawa juna sani na kasa da kasa, mai taken “Karfafa rawar da MDD ke takawa, tare da habaka ra’ayin cudanyar bangarori daban daban” a nan birnin Beijing.
Guo ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na yau da kullum da ya jagoranta a yau Talata, inda ya ce daukacin mahalarta taron na karawa juna sani sun yi imanin cewa, a halin da ake ciki, ya kamata a karfafa ayyukan MDD, da inganta hadin kai da hadin gwiwa, da kuma tinkarar kalubale daban daban da ake fuskanta a duniya.
Dangane da taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar raya kasar Sin na shekarr 2025 da aka gudanar a nan birnin Beijing kwanan baya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, taron shekara-shekarar na bana, ya samu halartar wakilan kasashen wajen sama da 750, kuma kamfanonin da suka halarci taron sun fito ne daga kasashe daban-daban, lamarin da ya nuna cewa, kamfanonin kasashen waje suna da kwarin gwiwar yin kasuwanci da Sin.
Game da rahoto mai taken “Hukumomin leken asiri na Amurka suna sa ido da satar bayanai da suka shafi tashoshin wayar salula na duniya”, wanda kawancen kamfanonin tsaro na Intanet na kasar Sin ya fitar a yau, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin ta nuna matukar damuwa game da munanan ayyukan da Amurka ke yi a yanar gizo da aka bayyana a cikin rahoton, ya kuma bukaci Amurka da ta gaggauta dakatar da hakan. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
Dubban mutane ne a birnin Amman babban birnin kasar Jordan suka gudanar da zanga-zanga bayan sallar Juma’a domin yin Allah wadai da sake dawo da laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.
A rahoton factjo, dubban mutane sun bayyana goyon bayansu ga al’ummar Gaza a wani gagarumin maci na wannan Juma’a.
Mahalarta tattakin sun yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan masallacin Al-Aqsa a cikin watan Ramadan.
A cikin wannan maci da aka gudanar bisa gayyatar Harkar Musulunci da kwamitin Tallafawa Falastinawa suka kira, dubban mutane sun halarta da suka hada da wakilai na siyasa, jam’iyyu, da kungiyoyin kwadago, da sauran jama’ar kasa, inda suka yi ta rera taken la’antar ayyukan zalunci na gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, da kuma kin amincewa da duk wata makarkashiyar da aka kulla domin korar Falastinawa daga yankunansu.
Haka nan Wadanda suka halarci tattakin sun yi Allah wadai da kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a zirin Gaza, tare da yin kira ga gwamnatocin kasashen Larabawa da na Musulunci da su dauki matakin gaggawa na dakatar da wannan aika-aikar da Isra’ila ke yi.
Mahalarta tattakin na nuna alhinin shahadar Abu Hamza, kakakin rundunonin Quds Brigade, sun yaba da karfin azamarsa da jajircewarsa, da sadaukar da ransa da jininsa saboda ‘yancin al’ummarsa.
Masu zanga-zangar sun kuma yi Allah wadai da cin amanar Amurkawa, wadanda suka bai wa makiya yahudawan damar soke yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma ci gaba da kashe al’ummar Gaza, tare da bayyana gwamnatin Amurka a matsayin wadda take daukar nauyin wannan laifi ta hanyar aika bama-bamai da makamai masu linzami ga Isra’ila domin kisan Falastinawa a zirin Gaza.