Aminiya:
2025-04-15@11:32:49 GMT

Super Eagles ta gamu da cikas a ƙoƙarin neman tikitin Gasar Kofin Duniya

Published: 26th, March 2025 GMT

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta gamu da cikas a ƙoƙarinta na neman yankar tikitin shiga Gasar  Kofin Duniya ta baɗi, bayan da ta tashi canjaras 1-1 da Zimbabwe.

Victor Osimhen ne ya fara ci wa Nijeriya kwallo a minti na 74 a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom.

Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo

Sai dai Zimbabwe ta farke ana daf da tashi a minti na 90 ta hannun ɗan wasanta na gaba, Taranda Chirewa.

Wannan sakamako na nufin cewa Nijeriya na matsayi na huɗu a rukunin C, inda Ghana ke gabanta a matsayi na ɗaya da kusan ratar maki shida bayan buga wasanni shida.

Wasan da Nijeriya za ta yi Bafana Bafana a watan Satumba, zai kasance mai matuƙar muhimmanci, la’akari da cewa ƙasar da ke saman kowane rukuni ne kaɗai ke samun damar zuwa Gasar Kofin Duniya.

A ranar Juma’a ce tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta doke Rwanda da ci 2-0 a birnin Kigali a wasannin neman gurbin shiga Gasar Kofin Duniya.

Ɗan wasan Nijeriya Victor Osimhen ne ya zura duka ƙwallayen biyu gabanin hutun rabin lokaci.

A lokacin Nijeriya ta koma matsayi na huɗu a cikin ƙasashe shida da ke Rukunin C bayan wasanni biyar-biyar.

Ƙasar da ta zama ta farko a kowane rukuni daga cikin rukunai tara na ƙasashen Afirka ne ke da tabbacin shiga gasar kofin na duniya, wanda a karon farko aka faɗaɗa zuwa ƙasashe 48.

Sai kuma za a zaɓi ƙasashe huɗu da suka fi ƙoƙari daga cikin waɗanda suka zama na biyu, sai su fafata wasan kifa-ɗaya-ƙwala na neman cike gurbi, inda waɗanda suka samu nasara za su iya samun damar shiga gasar.

Sauran wasannin da suka rage wa Super Eagles su ne na ranar 1 ga Satumba wanda Nijeriya za ta yi da Rwanda sai na ranar 8 ga Satumba tsakaninta da Afirka ta Kudu da kuma na ranar 6 ga Oktoba da za ta fafata da  Lesotho sai cikon na ƙarshe wanda za ta yi karon batta da Benin a ranar 13 ga Oktoba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Kofin Duniya Nijeriya Kofin Duniya shiga Gasar Gasar Kofin

এছাড়াও পড়ুন:

Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?

Manufar “ramuwar gayya” ba za ta daidaita gibin cinikin da kasar Amurka take fuskanta ba, illa ta daga farashin kayan da ake shigarwa kasar daga kasashen waje, da haddasa hadarin hauhawar farashin kaya a kasar, da kawo illa ga zaman rayuwar jama’ar kasar. A karshe Amurka ba za ta cimma burinta na zama a matsayin koli a duniya ba. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaƙin Neman Zaɓe A 2027: Ƙungiya Ta Nemi A Maye Gurbin Mai Magana Da Yawun Shugaban Ƙasa
  • Sin Na Maraba Da Masu Zuba Jari Domin Su More Damammakin Bunkasarta
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Alex Iwobi Ya Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74