Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa
Published: 26th, March 2025 GMT
Wani rahoto da aka fitar yau Talata, yayin zaman taron shekara-shekara na shekarar 2025, na dandalin tattaunawa na Asiya na Boao, ya nuna yadda kasar Sin ke ci gaba da kasancewa cibiyar rarraba hajojin da masana’antu ke sarrafawa.
Rahoton mai taken “Nazarin tattalin arzikin Asiya, da hadadden rahoton ci gaba na shekarar”, ya nuna yadda tun daga shekarar 2017, hada-hadar cinikayya ta duniya a fannin rarraba matsakaitan hajoji, ke kara dogaro kan kasar Sin sama da dogaronta ga yankin arewacin Amurka.
Bugu da kari, rahoton ya ce yamucin cinikayya da Amurka ta haifar a shekarar 2018, bai baiwa Amurkan wata nasara ta fuskar daga matsayinta, a hada-hadar rarraba hajojin da masana’antu ke sarrafawa ba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Kasar Oman A Matsayin Wajen Tattaunawa Na Gaba Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta sanar da cewa: Za a gudanar da zaman tattaunawa kan Shirin makamashin nukuliyar Iran zagaye na biyu ne a birnin Muscat na kasar Oman
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da cewa: Zaman tattaunawa zageye na biyu wanda ba na kai tsaye ba, tsakanin Iran da Amurka zai kasance ne a birnin Muscat fadar mulkin kasar Oman.
Baghaei ya yi watsi da rade-radin da ake yi kan inda za a gudanar da zagaye na biyu na tattaunawar kai tsaye tsakanin Iran da Amurka, Baghaei ya ce, “Bayan tuntubar juna, an yanke shawarar cewa birnin Muscat ne zai karbi bakwancin zagaye na biyu na shawarwarin, wanda za a yi a ranar Asabar mai zuwa.”
Wani abin lura a nan shi ne, an gudanar da shawarwari ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da manzon Amurka na musamman kan yankin gabas ta tsakiya Steve Witkoff dangane da batun Shirin makamashin nukiliyar Iran da kuma dage takunkumin da aka kakaba mata na rashin adalci da baya kan tubalin ka’ida. Tattaunawar ta samu halartar mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i da mataimakin ministan harkokin wajen Iran kan harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi, da mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da na kasa da kasa Kazem Gharibabadi, da manyan masu shiga tsakani kan batun dage takunkumi da batun Shirin makamashin nukiliya, da kuma kwararrun da suka dace.