Leadership News Hausa:
2025-03-27@23:05:20 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

Published: 26th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

1. Gibɗa a cikin Addini:
Wannan ya ƙunshi yin gasa a ibada kamar sallah, ko azumi, ko karatun Alƙur’ani, da sadaka, ko mutum ya so ya zama hamshaƙin mai kuɗi da zai rinƙa taimaka wa addini da bayin Allah. Ko kuma mutum ya nemi ya zama malami ko jagora a addini don ya koyar da mutane.

2. Gibɗa a cikin Duniya:
Wannan shi ne mutum ya so samun ilimi irin na wasu don ya amfanar da kansa da al’umma.

Ko kuma son ya zama attajiri ko ɗan kasuwa ko mai wata sana’a da zai rinƙa ba wa mutane horo saboda ya ga wani yana yi shi ma ya so ya ƙware ya taimaka domin samun lada a wurin Allah. Haka nan son samun shugabanci mai kyau domin jagorantar al’umma bisa gaskiya.

Manzon Allah (SAW) ya nuna irin wannanhassadarba laifi ba ce, inda ya ce: “Babu hassada sai a cikin abubuwa biyu: mutumin da Allah Ya ba shi ilimi, sai ya yi aiki da shi yana koyar da mutane, da kuma mutumin da Allah Ya ba shi dukiya, sai ya kashe ta a cikin hanyar da ta dace.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Bambanci Tsakanin Hassada da Gibɗa:

Idan mutum ya ga wani yana da ilimi, sannan ya so ya zama kamar shi ba tare da yana son ilimin wancan ya gushe ba, to wannan ita ce gibɗa. Idan kuma mutum yana jin haushin wani saboda Allah Ya ba shi wata ni’ima, yana kuma son ni’imar ta gushe daga gare shi, to wannan ita ce hassada wacce aka haramta.

Illon Mutum Ya Zama Maras Gibɗa:
Idan mutum bai da hali na gibɗa, to hakan zai haifar masa da:

• Rashin ƙwazo da son ci gaba a rayuwa.
• Rashin yin koyi da na-gari a al’umma.
• Watsi da neman ilimi da kwarewa a sana’a ko addini.
• Rashin gasa a ayyukan ibada, wanda zai iya sa mutum ya ja baya a addini.

Yadda Mutum Zai Zama Mai Gibɗa:

Idan mutjm yana son ya sami ta gari, to dole ne ya zamanto ya:

• Nemi arzƙi ta hanyar halal da nagartaccen ilimi mai amfani.
• Aiki tuƙuru don samun ci gaba, ba tare da cutar da wani ba.
• Yin addu’a don Allah Ya ba shi irin ni’ima da wasu ke da ita.
• Kauracewa hassada da kiyayya a zuciya.
Kallon wasu a matsayin abin koyi, ba makiya ba.

Allah Ya datar da mu. Amin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Allah Ya ba shi

এছাড়াও পড়ুন:

Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja

Ya ce, “Da misalin karfe 7:28 na safe ne wasu da ke sharar masallacin suka ga mutumin a kwance a cikin masallacin, sai suka yi kokarin tayar da shi domin su yi shara amma shiru.

 

Nan da nan, sai mutanen suka sanar da Musulman yankin lamarin, inda suka garzaya da shi zuwa asibiti, likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarsa.

 

Musa ya ce, daga bisani aka mika gawar marigayin ga ‘yan uwansa domin yi masa jana’iza.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
  • Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano
  • Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Yari A Libya – Gwamnati
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]