DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
Published: 26th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A duk lokacin da aka ce bukukuwa sun karato, akan samu sauyi a dukkan al’amura. Daya daga cikin irin wadannan sauyi da ake samu shi ne na farashin kayayyakin masarufi.
A wasu lokuta, akan samu tashin farashin irin wadannan kayayyaki, a wasu lokutan kuma akasin haka.
Shirin Daga Laraba na wannan makon zai tattauna ne kan farashin kayayyakin masarufi gabanin bikin sallah.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: farashin kayan masarufi
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ake fitar da Zakkar Kono
A yayin da watan Ramadan ɗin wannan shekara yake bankwana, ga abubuwan da malamai suka bayyana game da fitar da Zakkar kono, wato Zakatul Fidr ga duk wanda ke da hali.
Sahabi Abdullahi Ibn Abbas ya ruwaito cewa: “Manzon Allah (SAW) wajbata fitar Zakkar kono domin kankare kurakurai da yasassun maganganun da mai azumi ya yi, sannan sadaka ce ga miskinai.”
Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince AbokiDaga cikin hikimar bayar da ita, akwai sanya wa miskinai farin ciki ta hanyar samar musu da abin da za su ci a lokacin Ƙaramar Sallah.
Yadda ake fitarwaMutum zai fitar wa kansa da kuma waɗanda yake ciyarwa kamar mata, ’ya’ya da ma’aikata da sauransu idan Musulmai ne.
“Manzon Allah Ya wajabta fitar da zakkar kono ga babba da yaro, ’yantacce da bawa, daga cikin wadanda kuke ciyarwa,” kamar yadda Abdullahi bn Umar ya ruwaito a Hadisi.
Mai fitar da zakkar zai fara ne da fitar wa kansa, sannan sauran mutanen gwargwadon wajibcin ciyar da su a kansa.
Adadin da ake fitarwaKowanne mutum ɗaya za a fitar masa da Sa’i ɗaya, wato Mudun Nabi hudu.
Idan babu Sa’i ko Mudun Nabin awo, ana iya aunawa da tafin hannu.
Malamai sun ce Mudun Nabi ɗaya daidai yake da cikin tafin hannu biyu na matsakaicin mutum.
Abin da ake fitarwaAna fitar da zakkar kono ce daga nau’in ɗanyen abincin mutanen garin.
Ana fitarwa ne daga abin da ya ƙaru a kan abincin rana da yinin mai fitarwa da iyalansa a lokacin.
Lokacin fitarwaMalamai sun bayyana cewa ya halatta a fitar da zakkar tun daga ranar 28 ga Ramadan.
Hadisi ya nuna, “Abauullahi bn Abbas kan ba da ita da kwana ɗaya ko kwana biyu kafin ranar Sallah.”
Amma tana wajaba ne daga safiyar ranar Ƙaramar Sallah, a kuma gama kafin Sallar Idi.
“Wanda ya bayar kafin sallah to zakka ce karɓaɓɓiya, wanda ya bayar bayan sallah kuma to sadaka ya bayar kamar sauran sadakoki.”
Malamai sun ce haramun ne a jinkirta fitar da da ita ba tare da uzuri ba.
Waɗanda ake bai waHadisi ya nuna miskinai ake bai wa.
Wasu malamai na ganin ana iya ba da ita ga sauran mutanen da ake ba wa zakkar farilla (bayi, matafiya, masu bashi a kansu, masu aikin karbar zakka, masu aikin fisabilillahi, wadanda ake kwadayin su musuluntar).
Wanda aka ba wa zakkar shi ma zai fitar, idan har an samu ragowa.