HausaTv:
2025-03-29@08:32:56 GMT

Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta

Published: 26th, March 2025 GMT

Dakarun (RSF) sun sanya sabbin takunkumai kan isar da kayan agaji a yankunan da ke karkashin ikonsu, lamarin da ya kara ta’azzara matsalar ayyukan jin kai, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

Matsalolin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar RSF ke kokarin kafa gwamnatin daga bangarenta a yammacin kasar ammacin Sudan, duk da fatattakarsu sojojin kasar suka yi daga  babban birnin kasar, Khartoum, lamarin da ke barazana ga rarrabuwar kawuna a kasar da yaki ya daidaita.

Matakan da kungiyar ta dauka na hana gudanar da ayyukan agaji na barazana ga rayuwar dubban daruruwan mutane a yankin na Darfur, wadanda da dama daga cikinsu sun riga sun rasa matsugunansu sakamakon tashe-tashen hankula a baya.

A baya ma’aikatan agaji sun zargi mayakan RSF da wawushe kayan agaji a tsawon fiye da shekaru biyu da ake fama da tashin hankali a Sudan, lamarin da ke kara ta’azzara yunwa da cututtuka a  kasar.

Ma’aikatan agaji goma sha biyu, da suka yi magana da kamfanin dillancin labarai na Reuters, sun ce tun a karshen shekarar da ta gabata, kungiyar ta RSF ta fara neman karin kudade da kuma sa ido kan yadda ake gudanar da ayyuka, kamar daukar ma’aikatan cikin gida da tsaro, da irin tsarin da hukumomin da ke da alaka da sojoji ke amfani da su, da kuma kara tsaurara hanyoyin shiga.

A baya dai ba a bayar da rahoton wannan yunkuri na RFS ba,  amma kungiyoyin agaji na kasa da kasa sun fara ja da baya sakamakon matsanancin yanayin da ake ciki.

A cewar ma’aikatan agaji, yunƙurin da RSF ke yi ya kawo babban cikas ga ayyukansu, wanda ke nuni da yiwuwar fadawar miliyoyion mutane a cikin matsanancin hali na yunwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Za Ta Hana Baƙin Haure Shigowa Nijeriya Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Hana Baƙin Haure Shigowa Nijeriya Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Sudan ta Kudu : Ana tsare da Riek Machar a wani gida
  • Sudan : Janar al-Burhan Ya Shelanta ‘yantar Da Birnin Khartoum
  • JIBWIS Ta Raba Kayan Abinci Na Kimanin Naira Miliyan 9 Ga Marayu
  • Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin