Amurka ta shigo da sama da ganga miliyan biyu na man jiragen sama daga matatar Dangote a watan Maris.

Matatar ta tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, inda ta ce hakan ya tabbatar da “nagartar da ba ta misaltuwa” na kayayyakin matatar da kuma aminci da kasashen duniya suka bai wa matatar.

Duba daga  rahoton ma’aikatar sa ido kan zirga-zirgar jiragen ruwa ta Kpler, ta ce jiragen ruwa shida dauke da kusan ganga miliyan 1.7 na man jiragen sama daga matatar Dangote sun isa tashoshin jiragen ruwa na Amurka a wannan watan na Maris.

Wani jirgin ruwa, Hafnia Andromeda, ana kyautata tsammanin zai isa tashar Everglades a ranar 29 ga Maris tare da kusan ganga 348,000 na man jirgin sama daga matatar Dangote.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: daga matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kashe Mutane 38 Tare Da Jikkata Fiye Da 100 A Harin Da Ta Kai Lardin Al-Hudaidah Na Yemen

Adadin wadanda suka mutu sakamakon luguden wuta da Amurka ta yi kan tashar jiragen ruwan Ra’as Issa ta Yemen ya kai mutane 38

Ofishin kula da kiwon lafiya na lardin Al Hudaidah ya watsa rahoton cewa: Adadin mutanen da suka yi shahaida da wadanda suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan cibiyar man fetur ta Ra’as Issa da ke lardin Al-Hudaidah a yammacin kasar Yemen ya karu zuwa shahidai 38, tare da jikkata sama da mutane 100.

A yammacin jiya alhamis ne rundunar kawancen da Amurka ke jagoranta ta aikata wani mummunan laifi kan fararen hula a gundumar Al-Hudaidah da ke yammacin kasar Yemen.

Majiyoyin cikin gida sun shaidawa Al Masirah Net cewa: Jiragen yakin kawancen da Amurka ke jagoranta sun kai hare-hare 14 a kan tashar Ra’as Issa da ke gundumar, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu ma’aikata a wurin.

Majiyoyin sun yi nuni da cewa: An sake sabunta kai harin a wurin a yayin da jami’an tsaron farin kaya ke kokarin kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su, lamarin da ya yi sanadin shahadar jami’an tsaro da dama tare da jikkata wasu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kashe Mutane 38 Tare Da Jikkata Fiye Da 100 A Harin Da Ta Kai Lardin Al-Hudaidah Na Yemen
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  • Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba
  • Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
  • Yadiot Ahranot: Amurka Ta Bayyana Lokacin Ficewarta Daga Syria
  • DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo
  • Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia
  • Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS