Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
Published: 26th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya sanar da cewa har yanzu Iran ba ta mayar da martani kan wasikar da shugaban Amurka Donald Trump ya aike kan shirin nukiliyar Iran ba. Sai dai ya ce ana shirin mayar da amsa kuma za a mika ta hanyoyin da suka dace nan ba da jimawa ba.
Da yake magana a wani taron manema labarai na hadin gwiwa tare da ministan harkokin wajen Armeniya Ararat Mirzoyan a Yerevan, Araghchi ya nanata cewa Iran ba za ta shiga tattaunawa kai tsaye da Amurka ba a karkashin yanayin matsin lamba da barazanar soji, da kuma kakaba takunkumi.
Sai dai kuma ya tabbatar da cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa da kasashen Turai uku, tare da tabbatar da aniyar Iran ta fuskar diflomasiyya.
Wasikar wadda Trump ya sanar da aikewa da ita a ranar 7 ga Maris, an aike da ita ne zuwa ga jagoran juyin juya halin muslunci na Iran Ayatullah Sayyed Ali Khamenei, a daidai lokacin da gwamnatin Amurka ke ci gaba da aiwatar da matakai na matsin lamba a kan Iran, a daya bangaren kuma take nuna sha’awar yin shawarwari tare da kasar ta Iran.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran Esmaeil Baqaei ya fayyace cewa Tehran ba ta da wani shiri na bayyana wasikar a bainar jama’a, yana mai cewa ba lallai bane jita-jitar da kafafen yada labarai suka yada a game da wasikar ya zama gaskiya.
Za a yi martanin ne game da wannan wasiku ta hanyoyin diflomasiyya bayan yin cikakken nazari a kai, in ji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da Saudiyya
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa, Iran a shirye take yin aiki tare da Saudiyya a dukkanin bangarori, domin cin gajiyar al’ummomin kasashen biyu da ma duniyar musulmi, tare da yin ishara da cewa, dukkanin ci gaban da Iran ta samu a dukkanin bangarori na ilimin kimiyya da fasaha, a shirye take ta taimaka ma Saudiyya a wadannan bangarori.
Wannan na zuwa ne a lokacin da Ministan tsaro Yarima Khalid bin Salman dan uwa ga Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman ya gana da Ayatollah Khamenei a Tehran da yammacin jiya Alhamis don mika sakon Sarki Salman na Saudiyya.
Jagoran ya ce: “Mun yi imanin cewa dangantakar da ke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Saudiyya za ta kasance mai amfani ga kasashen biyu, kuma kasashen biyu za su iya kara kaimi domin karfafa juna.”
Ya kara da cewa “Yana da kyau ‘yan’uwa a yankin su hada kai da taimakon juna fiye da dogaro da wasu.”
Ayatullah Khamenei ya jaddada cewa fadada alaka tsakanin kasashen biyu ba abu ne da makiya za su yi farin ciki da shi ba, amma ya zama wajibi a yi hakan domin amfanin al’ummomin kasashen yakin da kuma al’ummar musulmi.
Ministan tsaron Saudiyya ya bayyana matukar jin dadinsa game Na zo Tehran ne da ajandar fadada alaka da Iran da kuma yin hadin gwiwa a dukkan fannoni,” in ji Yarima Khalid,
Ya kara da cewa “Kuma muna fatan wannan tattaunawar mai ma’ana za ta samar da kyakkyawar alaka tsakanin Saudiyya da Jamhuriyar Musulunci ta Iran fiye da kowane lokaci a tarihi.”