Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
Published: 26th, March 2025 GMT
Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II ya ce duk wani mai ƙoƙarin ja da hukuncin Allah to ba zai taba wanyewa lafiya ba.
Sanusi II ya ce duk wani mai ƙoƙarin kawo tazgaro ga zaman lafiyar Jihar Kano a ƙarshe aniyyarsa ce za ta koma kansa.
SSarkin ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan rediyon Premier da ke Kano, inda yake roƙon al’ummar jihar su zamo masu bin doka da oda, da kuma gudun aikata abubuwan da ka iya ta da hankali.
Kazalika ya bayyana masu ƙalubalantar kasancewarsa Sarki a matsayin masu yaƙi da nufin Allah, kuma a cewarsa hakan ba zai taɓa zame musu alheri ba.
Da yake jan hankalin Kanawan kan muhimmancin haƙuri da addu’a a wannan gaɓar, Sarkin ya ce turka-turkar da ake ciki game da masarautar Kano ba wai don shi ake yi ba, sai domin yaƙi da hukuncin Allah.
“Muna kira ga al’umma da su zamo masu bin doka da oda. Wannan rigimar ba da ni ake yinta ba, yaƙi ne da abinda Allah Ya ƙaddara.
“Ina roƙonku ku yi haƙuri ku dage da addu’a. Tabbas Allah Zai ci gaba da goya wa adalai baya.
“Wuta kuma ita ce karshen duk wani mai shirya wa Kano maƙarƙashiya. Allah Ya hana shi zaman lafiya.
“Muna roƙon Allah Ya kare kasarmu da rayukanmu. Da yardar Allah duk mai kokawa da hukuncin Allah ba zai gama da duniya lafiya ba,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Sarkin Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
Gwamnatin Kano ta sha alwashin hukunta masu shigar banza ko cudanya maza da mata a lokacin bukukuwan Sallah Karama da za a yi.
Gwamnatin ta bayyana hakan ne ta bakin shugaban Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Kano, Abba Almustapha a wata sanarwa da ta fitar mai dauke da sa hannun kakakin hukumar Abdullahi Sani Sulaiman, inda ta ce matakin yunkuri ne na gwamnatin domin tsaftace yadda gidajen wasanni da kidan DJ ke shagalin bikin Sallah.
Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa“A kokarin ta na yaki da rashin da’a tare tsaftace yadda gidajen wasanni da masu kidan DJ za su gudanar da shagalin bikin sallah a Kano, Hukumar tace fina-finai da Dab’i karkashin jagorancin Abba El-mustapha ta bayyana shirinta na saka kafar wando daya da duk wani gidan wasa ko mai kidan DJ da aka samu da rashin da’a a yayin gudanar da bikin sallah a Jihar.
Hukumar ta shirya wata tawaga ta musamman da za ta kewaya gidajen wasannin a bikin sallah karkashin kulawar Alh. Abubakar Zakari Garun Babba Daraktan Dab’i na Hukumar, domin sanya ido da tabbatar ba a bai wa masu shigar banza ko shaye – shaye damar shiga gidajen wasannin ba.
“Haka kuma, hukumar ta hana hada maza da mata a guri daya a yayin bikin sallar. Tawagar za ta yi aiki ne dare da rana daga ranar daya ga sallah har zuwa lokacin da za’a kammala bikin sallar domin cimma nasarar aikin da ta sanya a gaba.”
El-mustapha ya kuma yi gargadi ga masu gidajen wasanni da masu sana’ar DJ, da su yi biyayya ga dokokin hukumar sau da kafa domin gujewa fushinta.