Aminiya:
2025-04-18@15:36:45 GMT

Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa

Published: 26th, March 2025 GMT

Manjo-Janar Muhammad Inuwa Idris mai ritaya, Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Ayyuka na Musamman na Jihar Kano, ya yi murabus.

Wannan dai na zuwa ne bayan shafe watanni bakwai kacal da karɓar muƙamin.

Sakataren Labarai na Fadar Gwamnatin Kano, Mustapha Muhammad ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Larabar.

Sanarwar ta ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus ɗin Kwamishinan yana kuma yaba masa kan ƙwazon da ya yi wajen sauke nauyin da aka ɗora masa.

Kazalika, gwamnan yana yi wa Manjo-Janar Idris fatan samun nutsuwa da kwanciyar hankali a ritayar da ya yi.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar 16 ga watan Agustan bara ne aka rantsar da Manjo-Janar Muhammad Inuwa a matsayin kwamshinan, amma sai kimanin watanni biyar da suka gabata ne aka ƙirƙiro sabuwar ma’aikatar wacce aka danƙa ragamarta a hannunsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai

Paris St Germain ta kai zagayen daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai duk da rashin nasara da ta yi a hannun Aston Villa ranar Talata a Villa Park.

Aston Villa ta yi nasarar cin PSG 3-2, inda Tielemans da McGinn da kuma Konsa suka ci mata ƙwallayen a wasa falle na biyu a zagayen kwata fainal.

DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza

Ita kuwa ƙungiyar ta Faransa ta ci nata ƙwallayen ta hannun Hakimi da kuma Nuno Mendes.

PSG ta kai zagayen gaba da cin 5-4 gida da waje jimilla, bayan da ta yi nasarar cin 3-1 a makon jiya a Faransa.

Ita ma Barcelona da ke buga gasar La Liga ta kai matakin daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai ta bana duk da shan kashi da ta yi a hannun Borussia Dortmund.

Dortmund dai ta taka wa Barcelona burki, bayan wasa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba a dukkan kaka a bana.

Ƙungiyar ta Jamus ta doke ta Sifaniya da 3-1 a wasa falle na biyu na Gasar Zakarun Turai zagayen kwata fainal da suka fafata a Jamus ranar Talata.

Duk da haka Barcelona ta kai zagayen daf da ƙarshe sakamakon cin 5-3 gida da waje jimilla, bayan da ta ci 4-0 a makon jiya a Sifaniya.

Serhou Guirassy ne ya ci wa Dortmund ƙwallo uku rigis, wanda ta farko a bugun fenariti, sannan ya ƙara biyu bayan an dawo hutun rabin lokaci.

Barcelona ta zare ɗaya ne ta hannun Ramy Bensebaini, ɗan wasan Dortmund da ya ci gida.

Rabon da Barcelona ta yi rashin nasara tun cikin Disamba, bayan da Atletico Madrid ta ci ta 2-1, daga nan ta yi karawa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba har da canjaras huɗu daga ciki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
  • UEFA: Wasan Arsenal Da Real Madrid Ya Haddasa Rikici A Tsakanin Magoya Bayan Kungiyoyin A Kano
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai
  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • UEFA: Olmo Zai Wakilci Barcelona A Wasanta Da Dortmund