Ƙungiyoyin ƙwadago reshen Jihar Ribas sun yi barazanar ɗaukar mataki muddin gwamnatin Nijeriya ba ta janye dokar-ta-ɓacin da ta ayyana a jihar ba.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar gamayya da ƙungiyoyin ƙwadagon na NLC, TUC da JNC suka fitar a ranar 24 ga watan Maris.

Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa

Shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago na jihar sun nuna damuwa kan tasirin dokar-ta-ɓacin a kan tattalin arzikin jihar da kuma nuna rashin dacewar ta a hukumance.

A cewarsu, wannan matakin ya sanya an kasa biyan albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a jihar.

’Yan ƙwadagon sun bayyana cewa dakatar da zaɓaɓɓun jami’an gwamnatin jihar da rashin biyan albashin ma’aikatan keta haƙƙin bil’adama ne da ka iya ta’azzara matsalar tsaro da na tattalin arziki a jihar.

Sanarwar da ƙungiyoyin suka sanya wa hannun ta yi kira ga Tinubu da majalisar dokoki da kuma ɓangaren shari’a da su ɗauki matakan janye dokar nan take tare da mayar da gwamnan jihar da mataimakiyarsa da kuma ’yan majalisar jihar.

A cewar ’yan kwadagon, muddin ba a yi hakan ba nan da wani lokaci, za su ɗauki matakan da ka iya shafar tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan sanarwa na ƙunshe da sa hannun shugaban NLC na Ribas, Alex Agwanwor da takwaransa na TUC, Ikechukwu Onyefuru da kuma shugaban JNC, Chuku Emecheta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Ƙungiyoyin Ƙwadago Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Ɗanyen Man Da Ake Haƙowa A Ribas Ya Ragu

Aikin na tura danyen Man, ya kai akalla tsawon kilo mita 180 wanda a tura shi, daga wajen hako shi da ke a yankin Neja Delta.

danyen Man da Nijeriya ke hakowa, ya kai kasa da yawan wanda Hukumar OPEC ta iyakan ce, a watan Fabirairun  2025, wanda ya kai yawan Ganga  1,465,006 da ake hakowa a  kullum.

A yanzu dai, ana ci gaba da gudanar da bincike, domin a  gano musababbin abinda ya janyo fashewar man Bututun dan Man da irin asarar da aka tabka da kuma yawan adadin wadanda suka samu raunuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Masana’antu Da Cinikayya Na Kasa Da Kasa
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Dalilin Da Ya Sa Ɗanyen Man Da Ake Haƙowa A Ribas Ya Ragu
  • Duk Da Dokar ‘Yancin Samar Da Abinci: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Ƙaranci Abinci A Nijeriya
  • Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
  • Yobe Ta Bayyana Ɗaukar Matakan Tsaro A Lokacin Bikin Sallah
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara