Aminiya:
2025-03-29@13:02:07 GMT

Gobarar daji ta kashe mutum 24 a Koriya ta Kudu

Published: 26th, March 2025 GMT

Aƙalla mutum 24 ne suka rasu a wata gobarar daji mai muni da ta auku a tarihin Koriya ta Kudu baya ga mummunar ɓarna da ta haddasa.

Mukaddashin shugaban ƙasar ya sanar a ranar Laraba cewa wutar dajin ta rabu kashi daban-daban har fiye da goma tun ƙarshen mako, inda ta laƙume wasu yankunan kudu maso gabashin kasar.

Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

Har ila yau, ta kuma tilasta wa kusan mutum 27,000 ƙaurar gaggawa bayan ta datse tituna da kuma na’urorin sadarwa kamar yadda mazauna yankunan da ke neman tsira da rayukansu suka sanar.

Wani jami’in Ma’aikatar Kare Mutane ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa mutum 18 ne suka gamu da ajalinsu sakamakon wutar dajin baya ga waɗanda suka jikkata.

Sai dai daga bisani kafofin watsa labarai ciki har da BBC da CNN sun ruwaito cewa adadin waɗanda suka rasu ya kai 24 a dalilin gobarar.

A wani batun da ya shafi ƙoƙarin kashe wutar kuma wani jirgin sojin Koriya ta Kudun mai saukar ungulu ya faɗi da safiyar nan inda matuƙinsa ya rasu a ƙoƙarin dakile gobarar mai haddasa barna.

Alƙaluman da muhukunta suka fitar sun nuna cewa kimanin mutum 26 ne suka jikkata a dalilin gobarar dajin wadda ta ɗaiɗaita wani wurin bauta mai tsohon tarihi na mabiya addinin Buddha da ake kira Gounsa da ke yankin Uiseong.

Wani mutum tsaye yana kallon yadda gobarar dajin ta ɗaiɗaita wani wurin bauta mai tsohon tarihi na mabiya addinin Buddha da ake kira Gounsa da ke yankin Uiseong.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu wutar daji

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

NCDC, ta ce yawan masu kamuwa da cutar a bana ya fi na shekarar da ta gabata, inda a lokacin aka samu mutum 506 kacal.

Hukumar ta shawarci al’umma suke shan sha ruwa mai tsafta, su riƙa wanke hannu da sabulu, su ci abinci mai kyau, tare da tabbatar da tsaftar muhalli don guje wa kamuwa da cutar kwalara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Girgizar ƙasa ta hallaka sama da mutum 1000 a Myanmar
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand
  • An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Sudan ta Kudu : Ana tsare da Riek Machar a wani gida
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  • Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano
  • Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC