HausaTv:
2025-04-18@15:15:37 GMT

Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran

Published: 26th, March 2025 GMT

Bayan gazawar tattaunawar da hukumar ta IAEA ta yi da Tehran, babban daraktan hukumar Rafael Grossi ya jaddada muhimmancin komawa kan teburin shawarwari nan gaba don tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta ce tattaunawar da ta yi da wani babban jami’in kasar Iran a baya-bayan nan, ba a samu wani ci gaba kadan ba a cikin binciken nukiliyar da aka shafe shekaru ana yi kan kasar Iran, yana mai jaddada bukatar gaggauta warware takaddamar diflomasiyya da ke tsakanin Tehran da Washington.

A wata hira da Bloomberg babban darektan hukumar Rafael Grossi ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba zai koma Tehran domin ci gaba da tattaunawa da jami’an Iran. “Muna kan wani muhimmin mataki,” in ji Grossi, yana mai cewa wadannan tattaunawa za su iya taka muhimmiyar rawa a nan gaba.

Grossi ya kara da cewa shugaban kasar Amurka Donald Trump ya aike da wasika zuwa ga jagoran ruhin Iran, wanda ke nuni da bukatar cimma fahimtar juna da ke musanta yuwuwar Iran ta mallaki makamin nukiliya.

A sa’i daya kuma, Grossi ya jaddada bukatar shugabannin kasashen duniya su yi taka-tsan-tsan da kamewa, a daidai lokacin da ake ci gaba da tafka mahawara ta kasa da kasa game da bukatar dakile makaman nukiliya.

A cikin jawabinsa, Grossi ya bayyana cewa, duniya na fuskantar kalubale guda biyu: a bangare guda, akwai batutuwan da ba a warware su daga baya ba, a daya bangaren kuma, damar da ta kunno kai na cimma wata yarjejeniya nan gaba da za ta kai ga cimma matsaya kan batun nukiliyar Iran na dogon lokaci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya

Akwai kuma Sanata Adeniyi Adegbonire dan jam’iyyar APC daga mazabar Ondo ta tsakiya, Sanata Seriake Dickson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Bayelsa ta Gabas, Sanata Shehu Lawan Kaka, dan jam’iyyar APC, daga mazabar Borno ta tsakiya.

Sauran sun hada da; Sanata Banigo Ipaligo dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Ribas ta Yamma, Sanata Jarigbe Jarigbe dan jami’yyar PDP, daga Koros Riba ta Arewa, Sanata Ekong Sampson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom ta Kudu, Sanata Sani Bello dan jami’yyarAPC, daga mazabar Neja ta Arewa sai kuma Sanata Aniekan Bassey, dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom.

Majalisar ta kafa wannan kwamtin ne, biyo bayan kudurin da Sanata Aniekan Bassey na mazabar Arewa da Gabas daga Akwa Ibom, ya gabatar mata wacce ta yi daidai da dokokin 41 da 51.

Bugu da kari, a cikin kudurin da Sanata Bassey ya gabatar wa da Majalisar Dattawan ya yi gargadi da cewa, kutsen na ‘yan ta’addar daga kasar Kamaru, zai iya shafar tattalin arzikin jihar ta Akwa Ibom

Sanatan ya shedawa Majalisar cewa, yankin na Efiat, da ke a karamar hukumar Mbo a Akwa Ibom, na daga cikin yankin da aka bai wa kasar Kamaru a shekarar 1913, biyo bayan yarjejeniyar Anglo-German ko kuma a hukuncin da yarjejeniyar Babban Kotun Koli ta Duniya Duniya ta yanke a watan Okutobar 2002.

A nan, muna jinjiawa Majalisar ta Dattawa bisa kafa wannan kwamtin mai mambi tara, musamman domin kwamitin ya gudanar da bincike, kan wannan batun, na zargin kutsen ‘yan ta’addar na kasar Kamaru,a wannan yankin.

Sai dai, a wannan lokacin, yana da kyau a ci gaba da tsimayin sakamakon binciken da kuma shawarwarin da kwamtitin zai gabatar wa da Majalisar ta Dattawa kan wannan batun, domin sanin mataki na gaba da za a dauka.

Batu na maganar rikicin kasa, akasari, yana da wuyar lamari, wajen warware wa, musamman duba da cewa, Nijeriya da kasar Kamaru, kasashe ne, da suka gaji iyakoin kasa daga turawan mulkin mallaka, wadanda kuma, tun a baya, ba a fayyace yadda suke ba.

Bugu da kari, wannan lamari ne, mai matukar mahimmanci da ya shafi kasar nan.

Kazalika, ya zama waji, ‘yan Nijeriya su hada kansu, domin kare iyakokin kasar ga dukkan wata barazana, da za ta iya shafar kasar.

Sai dai, damuwar da akasarin ‘yan Nijeriya ke ci gaba da nunawa kan batun shi ne, na rashin mayar da hankali a siyasance, domin lalubo da mafita kan lamari irin wannan.

Mu a nan, muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kasance mai sanya ido sosai da kuma daukar kwararan matakai da za su kasance ba su kai ga zubar da kimar Nijeriya a idon duniya ba, wajen kare yiwa tattalin arzikin kasar nan.

Hakazalika, ya zama wajbi, Nijeriya ta tashi tsaye, wajen kare kasar daga dukkan wani na’ui na barazana daga kere domin kare kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya
  • Saudiyya da Iran sun jaddada aniyar fadada alakar soji a tsakaninsu
  • Iran Tana Daukan Tattaunawarta Da Amurka Da Muhimmanci Don Neman Warware Takaddamar Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Babban Jami’in Diblomasiyyar Iran Ya Je Birnin Mosco Don Isar Da Sakon Imam Khaminae Ga Putin
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • Kakakin Sojojin Kasa Na Dakarun IRGC Ya Ce Butun Tsaron Kasar Iran Da Karfin Sojojin Kasar Ba Abinda Tattaunawa Da Makiya Bane
  • Iran Ta Sanar Da Kasar Oman A Matsayin Wajen Tattaunawa Na Gaba Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya