Aminiya:
2025-03-29@14:21:16 GMT

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdulahi Usman, ya rasu

Published: 26th, March 2025 GMT

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, SP Abdulahi Usman, ya rasu bayan fama da doguwar jinya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi ne, ya tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago

Ya bayyana Usman a matsayin jajirtaccen ɗan sanda kuma gada tsakanin jami’an tsaro da al’umma.

“SP Usman ya shafe shekaru uku yana ƙarfafa hulɗa tsakanin ’yan sanda da jama’ar Taraba.

“Ƙwarewarsa, mutuntaka da jajircewarsa wajen neman adalci sun an samu tasiri,” in ji Adejobi.

Ya ƙara da cewa rasuwar Usman babban rashi ne ga rundunar ’yan sanda, abokan aikinsa da duk wanda ya san shi.

Sashen hulɗa da jama’a na ’yan sanda ya miƙa ta’aziyya ga iyalansa da kuma ‘yan uwansa, tare da yin addu’ar Allah Ya masa rahama.

Za a ci gaba da tunawa da Usman saboda sadaukarwar a aikinsa da ƙoƙarinsa na kyautata hulɗa tsakanin ’yan sanda da al’umma a Jihar Taraba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jinya Kakakin Yan Sanda Rashin lafiya rasuwa Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma

Wakilin kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Islamic Jihad a Tehran ya bayyana cewa: Ranar Qudus wata dama ce ta samar da hadin kai. A wannan rana al’ummar musulmi suna sabunta alkawarin da suka yi da Allah dangane da batun Palastinu.

Ranar Kudus tana hada kai tare da karfafa gwagwarmayar Musulunci a yankin.

Ya ci gaba da cewa, dukkanin bangarori na sun yi imanin cewa,  hanya daya tilo ta kubutar da Kudus da kuma ‘yantar da kasar Falasdinu ita ce goyon bayan Kudus da kuma tinkarar mamaye yankunan Falastinu da hakan ya hada da wannan masallaci mai alfarma da yahudawan sahyuniya suke yi.

Ranar Kudus ta duniya ita ce ranar da ke bayyana dukkan sharrin Amurka da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, kuma a wannan rana ne ake daga tutar ‘yanci da barranta daga zalunci, inji shi.

Ya kara da cewa, Wasu daga cikin shugabannin kasashen musulmi suna nuna halin ko-in-kula ga Palastinu da kuma halin da al’ummar Palastinu suke ciki, wanda kuma shirunsu nuna goyon baya ne ga zaluncin yahudawa a kan Falastinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
  • An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara
  • ’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu
  • Hadimin Gwamnan Kano, Abdullahi Tanka, Ya Rasu
  •  Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum
  • Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu