Aminiya:
2025-04-18@22:42:03 GMT

Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

Published: 26th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta ɗauki mataki na gaba wajen ƙirƙirar sabbin jihohi huɗu a Najeriya.

’Yan majalisa sun tattauna tare da amincewa da karatu na biyu na ƙudirorin da ke neman kafa jihohin Oke-Ogun, Ijebu, Ife-Ijesa, Tiga, Orlu, da Etiti.

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu

Waɗannan ƙudirori na daga cikin yunƙurin sauya kundin tsarin mulkin 1999.

Shugaban masu rinjaye na majalisa, Hon. Julius Ihonvbere, wanda ya gabatar da ƙudirorin, ya jaddada muhimmancinsu.

“Waɗannan ƙudirori suna nuna buƙatun yankuna daban-daban na ƙasa domin samar da ingantaccen shugabanci da rarraba albarkatu cikin adalci,” in ji shi.

Mataimakin Kakakin Majalisa, Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman, ya jagoranci kaɗa ƙuri’ar murya inda ƙudirorin suka samu amincewa.

An tura su zuwa kwamitin majalisa kan sauya kundin tsarin mulki domin ci gaba da nazari.

Ɗaya daga cikin masu ɗaukar nauyin ƙudirin, Hon. Ghali Mustapha Tijani, ya ce, “Kafa Jihar Tiga zai kusanto da gwamnati ga jama’a tare da haɓaka ci gaba.”

Ana buƙatar amincewar majalisun dokokin jihohi da na ƙasa kafin ƙirƙirar sabbin jihohin a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karatu Majalisar Wakilai Tsallakewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Kazalika, Injiniya Xie ya kara da cewa, a cikin rubu’in farko na bana, sashen masana’antu na kasar Sin ya taka rawar gani wajen samun ci gaba ba tare da tangarda ba sakamakon ingantuwar tsari da zurfafa ayyuka wajen samar da sabbin ginshikan bunkasa ci gaba mai inganci. (Abdulrazaq Yahuza Jere).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
  • Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Gwamnati Ta Ayyana 18 Da 21 Ga Afrilu A Matsayin Hutun Esta