Aminiya:
2025-04-18@18:25:17 GMT

Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano

Published: 26th, March 2025 GMT

Aƙalla mutum biyu ne suka rasu, yayin da wani ya jikkata a wani hatsarin mota da ya auku kusa da Sinimar Eldorado da ke kan titin zuwa Filin Jirgin Saman Malam Aminu Kano.

Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), ta tabbatar da faruwar lamarin.

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:15 na safiyar yau Laraba, inda ya haɗa wata babbar mota ƙirar DAF da babur ƙirar Jincheng.

Mai magana da yawun FRSC, Abdullahi Labaran, ya ce tuƙin ganganci ne ya haddasa hatsarin.

“Daga cikin mutum shida da hatsarin ya shafa, biyu sun rasu, yayin da ɗaya ya samu munanan raunuka,” in ji shi.

Jami’an FRSC sun isa wajen da hatsarin ya auku cikin minti uku sannan suka kai wanda ya jikkata zuwa Asibitin Murtala Muhammad domin samun kulawar gaggawa.

An kuma kai gawarwakin waɗanda suka rasu Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

An miƙa motocin da sauran kayayyakin da aka ƙwato zuwa ofishin ‘yan sanda na Gwagwarwa domin ci gaba da bincike.

FRSC, ta shawarci direbobi da su bi dokokin hanya tare da yin tuƙi cikin taka-tsantsan don kaucewa irin waɗannan haɗura.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano

A ƙarshe, wakilin Gwamna Abba Kabir Yusuf a taron, Sakataren Gwamnatin Jihar, Umar Faruk, ya nuna jin daɗinsa da ci gaban da aka samu wajen gyaran ɗaliban ta hanyar ilimi na yau da kullum, yana tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen ilimi na ‘yan gidajen yari a matsayin muhimmin mataki na dawo da su cikin al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • A Kalla Mutane 9 Ne Su Ka Yi Shahada A Gaza
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza