HausaTv:
2025-04-18@18:39:26 GMT

Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa

Published: 26th, March 2025 GMT

Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya amince da bukatar ma’aikatar shari’a na yin afuwa ga wasu fursunoni sannan kuma da rage yawan shekarun wasu na zaman gidan kurkuku.

Yin afuwar ga fursunonin dai ya zo saboda shiga sabuwar shekarar hijira shamshiyya ta 1404 da kuma karatowar karamar salla ra 1446.

Bugu da kari a wannan tsakanin ne ake bikin kafa tsarin jamhuriyar Musulunci na Iran.

Shugaban ma’aikatar shari’a ta Iran Hujjatul-Islam Wal Muslimin Gulam Muhsin Eji ne ya gabatar da bukatar neman afuwar ga fursunonin ta mutane 1526, wanda kuma ya sami amincewar jagoran.

A kowace shekara a lokutan bukukuwan addini da nasa ana yi wa fursunoni masu kananan laufuka afuwa, yayin da ake rage wa wasu tsawon wa’adin zamansu a gidan kurkuku.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato

Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya sanar da haramta kiwo da daddare tare da taƙaita amfani da babura a faɗin jihar sakamakon yawaitar hare-haren da ake kai wa a wasu sassan jihar.

A cikin wani jawabi da ya yi a jihar a ranar Laraba, Mutfwang ya bayyana hare-haren a matsayin “ayyukan ta’addanci” da ke da nufin tarwatsa mazauna yankin da kuma tauye hakkinsu na kasancewa cikin lumana a yankunansu.

Gwamnan ya kuma haramta safarar shanu cikin ababen hawa bayan karfe 7 na dare.

Ya kuma hana amfani da babura daga karfe 7 na yamma zuwa karfe 6 na safe a faɗin jihar har na wani tsawon lokaci inda ya ce umarnin zai fara aiki ne nan take.

Ya ce ” Ina jinjinawa masu ba da agajin gaggawa da jami’an tsaro bisa gaggarumin matakin da suka ɗauka, ina kuma gode wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya umurci jami’an tsaro da su tabbatar da adalci cikin gaggawa.”

Muftwang ya ce dole ne al’ummomi su ba da himma wajen kare kansu a cikin iyakokin da doka ta tanada.

Ya ce ”Ina kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin matasa da su sake farfaɗo da sintiri tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro. Dole ne mu haɗa kai don kare ƙasarmu, domin tabbatar adalci yayin da mu ke la’akari da kiyaye dokokin ƙasa.”

Aƙalla mutane 50 ne rahotanni suka ce an kashe bayan wasu ƴan bindiga sun kai hari ƙauyen Kimakpa da ke gundumar Miango a ƙaramar hukumar Bassa ta jihar a ranar 14 ga watan Afrilu.

Harin ya zo ne makonni biyu kacal bayan da wasu ƴan bindiga suka kashe mazauna ƙauyuka biyar a ƙananan hukumomin Bokkos da Mangu.

Hukumomin ƙasar dai na ci gaba da ƙoƙarin ganin sun daƙile hare-hare a jihar da aka daɗe ana fama da rikicin kabilanci da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Makiya Suna Adawa Da Fadada Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato
  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu