Kamfanin dillancin labarun “Reuters” ya nakalto cewa; An kai harinn ne wanda ya yi sanadiyyar mutuwa da kuma jikkatar wasu sojoji da dama a wasu sansanoni biyu dake Jihar Borno.

Mayakan kungiyoyin Boko Haram da Daesh suna kai wa fararen hula hare-hare a kasashen yammacin Afirka daga ciki har da Najeriya, inda suke kashe fararen hula da jami’an tsaro.

 Majiyar ta kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ta ce, kungiyoyin na “Da’esh’ da Boko Haram sun kai harin ne a yankin Wajiroko dake jihar borno, tare da cinna wuta a wurin da hakan ya yi sanadiyyar konewar kayan soja.

Wani soja ya bayyana cewa, a kalla 4 daga cikin sojoji ne su ka wanta dama sanadiyyar wannan harin, tare da jikkata wasu da dama daga cikinsu har da kwamanda.

Wasu madau dauke da makaman sun kai wani harin ne a garin Wolgu dake kan iyaka da kasar Kamaru, sai dai babu cikakken bayani akan yawan wadanda su ka kwanta dama ko su ka jikkata.

Wani daga cikin rundunar farar hula masu taimakawa sojoji a yaki da Bko haram din, mai suna Makinta Modu, ya fada wa manema labaru cewa, maharani sun kwace iko da sansanin sojan da su ka kai wa hari a Wajiroko.

Sai dai kuma an kawo  dauki daga sojan sama da misalin karfi 10;30 na dare, da su ka yi nasarar kashe masu dauke da makaman da dama.. Sai dai babu cikakken bayani akan ko sojojin sun sake kwato sansanin nasu da ya shiga hannun ‘yan ta’adda.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan

Mutane fiye 300 ne suka mutu a cikin kwanaki a wani kazamin fada a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan

Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta watsa rahoton cewa: Sama da fararen hula 300 ne aka kashe a wani kazamin fada na kwanaki biyu a yankin Darfur na kasar Sudan mai fama da rikici.

Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun kaddamar da hare-hare a ranakun Juma’a da Asabar a kan sansanonin ‘yan gudun hijira biyu da ke fama da matsalar yunwa a arewacin Darfur da kuma babban birnin da ke kusa, inda rahotannin farko suka nuna cewa sama da mutane 100 ne suka mutu, ciki har da yara 20 da ma’aikatan agaji tara, a cewar wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya.

A halin da ake ciki kuma, ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya (OCHA) ya sanar da samun karuwar adadin wadanda suka mutu a ranar Litinin, kamar yadda wasu majiyoyi na cikin gida suka tabbatar da hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 7 A Wani Sabon Hari A Benuwe
  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • Sin Kasuwar Duniya Ce Kuma Dama Ce Ga Kasa Da Kasa