Gwamnatin Iran Ta Kira Yi Al’ummar Kasar Da Su Fito Domin Halartar Jerin Gwanon Ranar Kudus
Published: 26th, March 2025 GMT
Mai Magana da yawun gwamnatin Iran malam Fatima Muhajirani ta yi ga al’ummar Iran da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin halartar jerin gwanon ranar Kudus ta duniya, wacce take fatan ganin ta taka rawa wajen taimakawa al’ummar Falasdinu.
Muhajirani wacce ta yi bayanin haka a wata hira ta tashar talbijin ta kuma kara da cewa; Gwargwadon yadda al’umma za su fito wajen yin jerin gwanon saboda hadakar da ake da ita a tsakanin al’ummar Iran da Falasdinawa ta fuskokin addini da al’adu, da kuma tarayya akan manufofin juyi, tasirin haka zai fi fitowa.
Malama Fatima Muhajirani ya kuma ambato maganar Imam Khumaini ( r.a) akan fatansa na ganin an sami fitowa mai yawa domin karfafa al’ummar Falasdinu.
A na gudanar da jerin gwanon ranar Kudus ta kasa da kasa ne a kowace ranar juma’ar karshe ta watan Ramadan mai alfarma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Litinin, 31 ga watan Maris, da Talata, 1 ga watan Afrilu, a matsayin ranakun hutun ƙaramar salla.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar, Magdalene Ajani, ya fitar a ranar Laraba.
Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasuYa taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira a gare su da su ci gaba da halaye nagari da suka koya a watan.
Haka kuma ya jaddada muhimmancin soyayya, yafiya, da haɗin kai wajen gina al’umma.
Tunji-Ojo, ya buƙaci ’yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaban ƙasa.
Ya yi fatan cewa bukukuwan salla za su ƙara haɗin kai tsakanin mutane duk da bambancin addini da ƙabilanci da ake da su.
Haka kuma, ya yi kira ga jama’a da su yi bukukuwan ta hanyar tunawa da mabuƙata, ta yadda za a taimake su.
A madadin Gwamnatin Tarayya, ministan ya aike da saƙon fatan alheri ga dukkanin Musulmi tare da addu’ar Allah Ya sanya farin ciki a zukatan kowa.