HausaTv:
2025-04-18@18:34:44 GMT

HKI Ta Kai Hare-hare A Falasdinu Da Kasar Lebanon

Published: 26th, March 2025 GMT

Sojojin mamayar HKI sun kai sabbin hare-hare a wasu yankuna na gabashin kasar Lebanon, adaidai lokacin da take ci gaba da kai wa yankin yammacin kogin Jordan wasu gare-haren.

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa; Sojojin mamayar sun kame Falasdinawa 5 a garin al-Khalil dake kudancin yammacin kogin Jordan.

Haka nan kuma sun kama wasu Falasdinawa 8 a garin Nablus.

A garin Bireh da wasu yankuna na Ramallah, sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren a yau Laraba.

A cikin watannin bayan nan, sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinwa 79 a cikin yankin yammacin kogin Jordan, tare da tilastawa mazaunan gidajen kusan 40,000 yin hijira.

A ranar 22 ga watan Maris ne dai jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a gargruwan Lebanon da su ka hada, Nabi Shit, Hermel, da wasu garuruwan da suke a yankin Bika. Haka nan kuma sun kai wasu hare-haren a garin Deir Qanun.

Tun daga fara yaki akan Gaza, sojojin HKI sun kashe Falasdinawan da sun haura 50,000, yayin da wani adadin da ya kai mutane113,000 su ka jikkata.

A can yankin Gaza ma, sojojin na HKI suna cigaba da kai hare-hare wanda ya yi sanadiyyar samun shahidai da dama.

Hare-haren na sojojin mamaya ya shafi garin Khan-yunus dake kudancin Gaza, haka nan kuma a garin Rafaha dake kan iyaka da kasar Masar.

Da safiyar yau Laraba kadai Falasdinawa 11 ne su ka yi shahada, daga cikinsu da akwai kananan yara 5.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu

Mai Magana da yawun kakakin babban magatakardar MDD Steven Dujarric ya nuna damuwa akan sanar da kafa wata gwamnati ta daban da shugaban rundunar daukin gaggawa Hamidati Duklu ya yi a shekaran jiya Laraba.

Shugaban rundunar kai daukin gaggawar ta Sudan wanda yake fada da sojojin kasar ya shelanta kafa sabuwar gwamnati wacce ya ce za ta kasance ta zaman lafiya da hadin kai ce.

Hamidati wanda ya gabatar da jawabi a lokacin da ake tunawa da zagayowar cikar shekaru 3 da fara yaki a kasar ta Sudan, ya kuma ce; A halin yanzu suna Shirin buga kudaden Sudan na daban, da kuma samar da wasu muhimman takardu na aikin gwamnati.

Wannan sanarwar daga shugaban rundunar kai daukin gaggawar ta Sudan yana zuwa ne bayan da sojojin Sudan su ka kori mafi yawancin mayakansa daga birnin Khartum da kuma wasu muhimman wuraren a kasar ta Sudan.

A watan da ya shude ne dai shugaban dakarun kai daukin gaggawa na Sudan din ya halarci wani taro a kasar Kenya da ya shelanta kafa gwamnatin bayan fage tare da wasu kungiyoyi da suke goya masa baya.

Shi dai Hamidati yana fuskantar zarge-zarge daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasa da kasa akan aikata laifuka da su ka hada da yi wa mata fyade da cin zarafin kananan yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato
  • A Kalla Mutane 9 Ne Su Ka Yi Shahada A Gaza
  • Kakakin Sojojin Kasa Na Dakarun IRGC Ya Ce Butun Tsaron Kasar Iran Da Karfin Sojojin Kasar Ba Abinda Tattaunawa Da Makiya Bane