Aminiya:
2025-04-18@21:54:21 GMT

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe

Published: 27th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 27 da buhunan shinkafa 300 ga mutanen da gobara ta shafa a ƙananan hukumomi uku da ke mazaɓarsa a Jihar Yobe.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Machina, Nguru, da Yusufari.

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Sanata Lawan, ya jajanta wa mutanen da suka yi asarar dukiya sakamakon gobarar.

Ya ce haƙƙinsu ne su taimaka wa juna, kuma zai ci gaba da ƙoƙari don ganin cewa wadanda abin ya shafa sun samu tallafin da ya dace.

Ya bayyana cewa wannan tallafin zai ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, tare da taimaka musu, su farfaɗo daga ɓarnar da gobarar ta yi musu.

A cewarsa, an ware Naira miliyan 12 da buhunan shinkafa 150 ga Ƙaramar Hukumar Machina, wanda za a raba a garuruwan Ngabarawa, Dole, Ghana, da Damai.

Ƙaramar Hukumar Nguru, za ta karɓi Naira miliyan biyar da buhunan shinkafa 50, wanda za a raba wa al’ummar Askema da Mirba.

Ƙaramar Hukumar Yusufari, za ta samu Naira miliyan 10 da buhunan shinkafa 100, wanda za a raba wa mutanen Tulo-Tulo da Isufuri.

Sanata Lawan, ya buƙaci gidauniyar SAIL Foundation, wacce ke kula da rabon tallafin, da ta tabbatar da gaskiya da adalci wajen raba wa waɗanda suka cancanta.

Ya kuma yi addu’a Allah Ya ba waɗanda abin ya shafa ikon jure wannan jarabta da sauƙi a gare su, musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Sanata Ahmed Lawan da abin ya shafa Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda

Mako guda bayan rage farashin fetur da Naira 45, matatar mai ta Dangote ta sake karya farashin man ga ‘yan sari da ragin Naira 30 duk lita.

Aminiya ta rawaito cewa matatar na sayar da man ne a ranar Laraba akan ₦835, saɓanin makon da ya gabata da ta sayar da shi akan ₦865 bayan rage farashin daga ₦880 da ta sayar a makon da ya gabata.

Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya

Hakan dai na nufin a cikin makonni shida, Dangoten ya rage farashin fetur ɗin sau uku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • ‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati
  • Kamfanonin Lantarki Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Bashin Naira Tiriliyan 4