Aminiya:
2025-03-29@20:32:20 GMT

Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu

Published: 27th, March 2025 GMT

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Rediyo ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu.

Ya rasu ne a ranar Laraba 26 ga watan Maris, 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4 Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Kakakin Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya tabbatar da rasuwar cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta bayyana marigayin a matsayin ƙwararren ɗan jarida da ya taka rawar gani wajen inganta harkokin sadarwa a jihar.

Za a yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin yau Laraba a Filin Masallacin Galadanchi da ke kusa da gidan Galadiman Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya nuna alhininsa kan rasuwar Galadanci, tare da bayyana irin rawar da ya taka a gwamnatinsa.

“Rasuwar Abdullahi Tanka Galadanci babban rashi ne ga gwamnatina da Jihar Kano baki ɗaya.

“Za a yi rashinsa saboda jajircewarsa da ƙwazon da ya nuna wajen inganta harkokin sadarwarmu,” in ji gwamnan.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalansa, ’yan uwa da abokan arziƙi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Kano rasuwa ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya

kungiyar ta koka kan cewa bai dace a yi amfani da EFCC wajen kamun Jami’an gwamnatin jihar Bauchi da nufin nuna yatsa wa Gwamna Bala Muhammad wanda ya kasance mai fitowa da hakikanin gaskiyar halin da talakawa ke ciki da nema musu hakkinsu daga wajen shugaban kasa.

kungiyar ta lura da cewa in ana amfani da irin wannan salon lallai za a samu nakasu wajen kyautata demukradiyya a kasar nan domin mutane da dama za su yi shiru kan abubuwan da suke tafiya ba daidai ba domin gudun musgunawa.

Eyes on Democracy ta kuma nuna shakku kan yadda aka kama Akanta Janar din a lokacin da yake halartar taron FAAC a Abuja, inda ta bayyana cewa hukumar EFCC ba ta gayyace shi ba balle ya ki zuwa da har za a dauki matakin kamashi.

“Babu ko shakka cewa Gwamna Bala Mohammed yana tafiyar da harkokin kudi da dukiyar jihar cikin tsanake da gaskiya, a karkashin shugabancinsa jihar Bauchi na samun ci gaba da ba a tava ganin irinsa ba kuma cikin sauri a sassa daban-daban,” kungiyar ta shaida.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Nijeriya, kungiyoyin farar hula, da sauran kasashen duniya da su lura da wadannan ayyukan da ba su dace da tsarin dimokradiyya ba, su bijirewa duk wani yunkuri na mayar da hukumar EFCC dandalin cin zalin siyasa.

Bugu da kari, kungiyar ta yi kira ga hukumar EFCC da ta yi aiki bisa doka, sannan ta bukaci da a gaggauta sakin Akanta Janar din, idan har akwai zarge-zarge na gaskiya da ake yi masa, kungiyar ta dage cewa a bi su kamar yadda doka ta tanada.

“Muna tsayawa tsayin daka da Gwamna Bala Mohammed da dukkan masu fada a ji na gaskiya da adalci a Nijeriya. Babu wata barazana da za ta hana a gudanar da gangamkn na tabbatar da dimokuradiyya, gaskiya da rikon amana,” in ji ƙungiyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
  • Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka
  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  • Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu