Sanarwar ta umarci dukkanin waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar aiki ga Sakatarorin ma’aikatun da suke jagoranta.

Idan babu Sakatare, sai miƙa ragamar ga babban Darakta mafi girma ko Shugaban Harkokin Gudanarwa.

Wannan umarni zai fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare.

Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Dakatarwa Jihar Ribas Muƙaman Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya fitar da wata sanarwa mai ƙarfi game da yiwuwar dawowar wasu shugabannin siyasa cikin jam’iyyar. A lokacin ganawar da manema labarai a Kano, Abbas ya bayyana cewa APC ba za ta karɓi mutane da hukumomin yaƙi da cin hanci kamar EFCC da ICPC ke bincike ba.

Wannan sanarwa ta zo ne a yayin da jita-jita da ake cewa wasu daga cikin mambobin jam’iyyar NNPP, musamman waɗanda ke cikin rukuni na Kwankwasiyya, suna duba yiwuwar komawa APC.

El-rufa’i Ba Zai Halarci Taron Jam’iyyar APC Na Kasa Ba, Kuma Ganduje Na Nan A Shugabanci  NNPP Ta Mutu, Kwankwaso Zai Sake Dawowa APC – Ganduje

Abbas ya bayyana cewa duk wanda ke son dawo wa jam’iyyar dole ne ya nemi afuwa daga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, bisa maganganun cin mutunci da aka yi a baya akan su da jam’iyyar.

Masu fashin baƙin siyasa na ganin cewa wannan magana ta Abbas tana nufin shugaban Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ake zargin yana cikin tattaunawar yiwuwar sauya sheƙa. Wannan furucin na shugaban APC na Kano ya janyo muhawara game da yadda siyasa da daidaiton ra’ayi za su iya faruwa a cikin tsarin siyasar Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin
  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Cambodia
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Masu Jan Hankalin Xi Jinping” A Kasar Malaysia
  • Kamfanonin Lantarki Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Bashin Naira Tiriliyan 4
  • Matashin Da Ya Ƙware Wajen Kashe Mutane Da Ƙwace Ya Miƙa Kansa Ga ‘Yansanda A Kano