Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
Published: 27th, March 2025 GMT
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
Fashin Baƙi:
Wannan magana ta Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa tana bayani ne a kan istigfari ( wato nema gafarar Allah) da sakamakonsa a rayuwar mutum. Domin fahimtar wannan tasa dalla-dalla, zan yi bayani a matakai uku:
Ma’anar Istigfari da Muhimmancinsa:
Istigfari na nufin neman gafarar Allah Ta’ala bisa zunubai da aka aikata.
” sai na ce: Ku nemi gafarar Ubangijinku, lalle Shi Ya kasance Mai ywana gafara ne” Suratu Nuh aya ta 10.
Manzon Allah (S.A.W) yana yawaita istigfari fiye da sau saba’in a rana, kamar yadda hadisi ya tabbatar da haka a cikin Sahihul Bukhari da Muslim..
Sakamakon Istigfari a Bisa Maganar Ibnu Juzai:
Ibnu Juzai yana bayani ne cewa istigfari yana da tasiri a rayuwar mai neman gafara, kuma sakamakonsa yana bayyana a cikin:
Tsayuwa Kan Taƙawa:
Taƙawa tana nufin kiyaye umarnin Allah da guje wa haninsa wato nisantar saɓa masa. Idan mutum yana neman gafarar Allah da gaske, hakan yana ƙarfafa tsoron Allah a zuciyarsa, wanda ke hana shi komawa ga zunubi. Allah Ta’ala Yana cewa:” Kuma ku tuba ga Allah gaba ɗayanku ya ku mummunai domin ku rabauta” Suratun Nur aya ta 31.
Kiyaye Sharuddan Tuba:
Tuba tana da sharuɗa guda uku, idan zunubin ba ya da alaƙa da wani bawa, to sharuɗan guda uku ne, idan kuma yana da alaƙa da wani, to sharuɗan hudu ne kamar haka:
1. Nadama bisa abin da aka aikata.
2. Barin zunubin nan take ba tare da jinkiri ba.
3. Ƙudirin kada a koma ga zunubin nan gaba.
4. Idan ya shafi wani mutum, sai a biya shi haƙƙinsa.
Idan mutum yana istigfari ba tare da kiyaye waɗannan sharuɗa ba, to istigfarinsa ba zai ba yi mass tasiri sosai ba.
Inkarin Saɓo da Zuciya:
Wannan yana nuna cewa zuciyar mai istigfari tana ƙin saɓo kuma tana jin haushin zunuban da aka aikata a baya. Wannan na nufin istigfari na gaskiya yan ƙarfafar bawa a kan aibata saɓo da jin nauyin aika shi. Hakan yana nufin istigfari yana gina halin mutumin da ya fahimci girman zunubi, kuma hakan yana hana shi sake aikata shi.
Muhimmancin Wannan Magana a Rayuwa:
Maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa:
• Istigfari ba kawai furuci ba ne, yana da tasiri ga zuciya da hali.
• Dole ne istigfari ya kasance tare da takawa da gujewa sabo.
• Kiyaye sharuɗan tuba yana tabbatar da cewa istigfarin mutum ya dace da shari’a.
A taƙaice, Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana jaddada cewa istigfari na gaskiya yana haifar da tsayuwa a kan addini, da kiyaye dokokin Allah, da gujewa komawa ga zunubi. Wannan yana nufin cewa nema gafarar Allah ba wai magana ce ta fatar baki kawai ba, sai da aikin zuciya da na gaɓɓai.
Allah ya sa mu kasance cikin masu istigfari na gaskiya!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan gafarar Allah Istigfari na istigfari na a istigfari
এছাড়াও পড়ুন:
Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
Gwamnatin jihar Neja za ta fara gudanar da zirga-zirgar jiragen sama daga sabon filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu da aka kaddamar a Minna, tare da kamfanin Overland Airways Limited.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da zirga-zirgar jiragen sama na Overland, Captain Edward Boyo ya raba wa manema labarai a Minna, babban birnin jihar Neja.
Ya bayyana cewa an shirya fara jigilar jiragen a ranar 23 ga Afrilu, 2025, wanda zai hada Minna zuwa Abuja da Legas, manyan biranen siyasa da kasuwanci na Najeriya.
Kyaftin Boyo ya bayyana cewa, haɗin gwiwa da kamfanin na Overland Airways—kamfanin jiragen sama masu zaman kansu mafi dadewa a Najeriya—yana wakiltar wani muhimmin ci gaba na aiwatar da tsarin raya ababen more rayuwa na Gwamna Bago da kuma sanya jihar Neja a matsayin cibiyar sa hannun jari, kasuwanci, da yawon buɗe ido.
“Mun yi farin cikin zabar mu a matsayin kamfanin da zai kaddamar da wannan aiki mai dimbin tarihi, “Wannan hidimar tana kara jaddada kudurinmu na fadada hanyoyin sadarwa a fadin Najeriya da kuma hada hannu da gwamnatoci masu hangen nesa kamar jihar Neja domin kawo ci gaba kusa da jama’a, saboda haka muna jinjina wa Gwamna Bago da tawagar NNA kan wannan jajircewa da kawo sauyi.” Ya bayyana.
Tun da farko, babban jami’in gudanarwa na hukumar ta NNA, Alhaji Liman Katamba Kutigi ya ce, “Wannan shirin ya wuce hanyar jirgin sama— gada ce ta samun dama. Ta hanyar hada kai da kamfanin jiragen sama na Overland, muna kafa wani sabon tsari na hada-hadar zirga-zirgar jiragen sama na yankin, tare da aminci da tasirin tattalin arziki.
A cewarsa, wannan shi ne mafarin babban ajandar mayar da jihar Neja a matsayin wata babbar mai taka rawa a harkokin sufurin jiragen sama da na Najeriya.”
A cewar tsare-tsare Tsarin Jirgin kamar haka; Minna – Lagos – Minna: Litinin, Laraba, Juma’a, yayin da ita
Tashi daga Legas zuwa Minna: 8:00 na safe
Tashi daga Minna zuwa Legas: 3:00 na yamma
Minna – Abuja – Minna: Litinin, Laraba, Juma’a da kuma tashi daga Minna zuwa Abuja: 9:30 na safe haka kuma ya tashi daga Abuja zuwa Minna: 2:00 na rana.
Saboda haka, Overland Airways an san shi da kyakkyawan yanayin tafiye-tafiye na yanki, zai yi amfani da waɗannan jiragen ta hanyar amfani da sabon jirginsa na Embraer E-175, kuma kamfanin jirgin ya kiyaye IATA Operational Safety Audit (IOSA) rajista tun 2015 kuma yana aiki da rundunar jiragen ruwa da suka haɗa da Embraer jets, ATR-42s, ATR-42s, ATR-72s da kuma ATR-70D.
PR ALIYU LAWAL.